Thursday, July 16
Shadow

Ina sane da ana shan wahala a Najeriya amma ba laifina bane>>Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince da cewa ya yadda ana shan wahala a Najeriya.

Tinubu ya bayyana hakane a ganawar da yayi da tsaffin shuwagabannin majalisar tarayya wanda Ken Nnamani ya jagoranta.

Ya bayyana cewa sakacin gwamnatocin da suka gabata ne ya jefa kasar a halin da take ciki.

Yace amma da hadin kai da aiki tare za’a samu ci gaba a Najeriya.

Tun bayan da shuyaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ya cire tallafin man fetur ne dai Najeriya ta shiga cikin halin matsin tattalin arziki wanda har yanzu bata fita ba.

Karanta Wannan  Ba nasarar Allah da Annabi kasar Congo ta yi akan mu ba, Sihiri suka mana>>Inji Kocin Najeriya, Éric Chelle bayan Kasar Congo lallasa Najeriya da ci 4-3 wanda hakan ya hana Najeriya kaiwa ga buga gasar cin kofin Duniya ta 2026

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *