Friday, December 26
Shadow

Kalli Bidiyo: Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya bayar da Umarnin yin Azumi a jiharsa dan Rokon Allah ya magance matsalar tsaro

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya bayar da Umarni a jiharsa ta Borno cewa mutane su tashi da Azumi dan a roki Allah ya magance matsalar tsaro a jihar.

Gwamnan yace za’a tashi da Azuminne ranar Litinin, 24 ga watan Nuwamba inda yace a hada da addu’o’i musamman saboda dawowar Kungiyar Bòkò Hàràm inda take ci gaba da kai hare-hare a jihar

Wannan na zuwane Kwanaki kadan bayan da Kungiyar ta Bòkò Hàràm ta Khashye Janar din Soja, Muhammad Uba.

Karanta Wannan  Lamari Ya Munana: Kungiyar PENGASSAN dakatar da ayyukan tace mai a matatar Man fetur ta Dangote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *