
Matan sojojin da aka kama da zargin cewa sun shirya yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki sun fito zanga-zanga.
Sun fito inda suka rika bayyana damuwarsu bisa jagorancin Omoyele Sowore.
Sowore ya bayyana cewa da yawa iyalan sun ce babu wata maganar juyin mulki da mazajensu ke da hannu akai.
Kawai wasu manyan sojoji ne ke son farantawa shugaban kasa rai.