
Wasu ‘yan PDP daga Kudancin Najeriya sun baiwa Atiku Abubakar bakin cewa ya hakura da maganar tsayawa takara a shekarar 2027 ya barwa dan kudu.
Sun ce ba ma Atiku kadai ba, duk wani dan Arewa kamata yayi ace ya hakura da tsayawa takara a barwa dan kudu ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2027.
Kungiyar tace dama can Atiku ne ya fara jawowa jam’iyyar PDP koma baya a shekarar 2014 inda ya jagoranci gwamnoni 5 suka fice daga jam’iyyar suka koma APC suka juyawa Goodluck Jonathan baya.
Shugaban kungiyar, Dennis Shima ne ya fadi haka inda yace ya kamata a bar dan kudu ya kammala shekara 8 kamar yanda Buhari yayi