
Rahotanni sun bayyana cewa, Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio na can asibiti a birnin landan inda yake jinya.
Hutudole ya ruwaito muku jiya cewa, Akpabio ya yanke jiki ya fadi ne inda Sabbin Rahotannin da muka sau suka ce Dangote ya bayar da jirgi aka tafi dashi Landan inda yake jinya.
Kuma mun samu cewa Lamarin ya farune ranar 10 ga watan Disamba, kamar yanda Sahara Reporters ta ruwaito.
Hutudole ya fahimci cewa, Likitoci sun ce Aiki ne yawa Akpabio yawa shiyasa wannan lamari ya sameshi, da haka suke bashi shawarar ya ajiye aiki ya koma ya kula da lafiyarsa.
Akpabio dai an ganshi a karshe a zauren majalisar tun ranar da majalisar ta amincewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aika da sojoji kasar Benin Republic.