
Rahotanni sun bayyana cewa kasar Israela ta amince da matakin kwace gaba dayan yankin Gaza ya koma karkashin mulkinta.
Dan hakane ta kirawo duka sojojinta da suka yi ritaya dana karta kwana dan gudanar da wannan gagarumin aikin.
Israela dai bata bayyana zuwa yaushene zata rike zirin na gaza ba watau saidai abinda Allah yayi.
Kasar ta Israela tace a wannan sabon mataki zata bari a shiga da kayan agaji cikin Gaza amma zata saka ido ta tabbatar basu fada hannun kungiyar Hamas ba.