Saturday, September 12
Shadow

Ko makaho yasan ina aiki a kasarnan>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Ko mahako yasa yana ayyukan ci gaba a Najeriya.

Shugaban ya bayyana hakane yayin kaddamar da titin Apo-Wasa dake Abuja.

Shugaban yace Najeriya haka take shekarun 1960 ko kuwa haka take a shekaru 3 da suka gabata? Amma ‘yan Adawa babu me yabawa sai suka.

Shugaban ya baiwa ‘yan Adawa shawarar su mayar da hankali wajan gyara matsalarsu kamin zaben 2027 dan kada wani ya zargeshi da yin magudi.

Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ne ya wakilci shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a wajan kaddamar da titin.

Karanta Wannan  Ji yanda Gwamnan jihar Kebbi ya bayyana cewa DSS sun gargadesu game da yunkurin dauke daliban makarantar 'yanmata ta MAGA, kuma sun kai jami'an tsaro amma Mintuna 30 kamin tshageran daji su kwashe daliban sai jami'an tsaron suka bar makarantar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *