
Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya baiwa ‘yan Najeriya shawarar su rika yin sadaka inda yace tana jawo Alkhairai da yawa.
Tsohon shugaban kasar ya bayyana hakane ranar Juma’a a wajan kaddamar da fara gyaran wani masallacin dake Kobiti, Abeokuta, jihar Ogun.
An kaddamar da fara shirin gyaran masallacin a Dakin karatu na Obasanjon dake Abeokuta.
A jawabin da yayi lokacin bude kaddamar da aikin, Obasanjo yace sada wadda kowane mutum na iyayi ba tare da la’akari da addini ko karfin tattalin arziki ba, tana jawo Alkhairai da yawa.