Friday, December 5
Shadow

Kwanan nan mutane zasu daina yadda da kariyar gwamnati zasu fara tashi tsaye suna kare kansu>>David Mark

Tsohon Kakakin majalisar Dattijai, Sanata David Mark ya bayyana cewa, Kwanannan mutane zasu daina yadda da cewa gwamnati zata karesu inda zasu fara tashi tsaye suna kare kansu.

Mark ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Paul Mumeh inda yace lamarin tsaro ya kazance.

Ya jawo hankalin gwamnati data dauki mataki ko kuma nan gaba kadan mutane zasu fara tashi tsaye suna kare kansu.

Ya bayyana hakane a yayin da aka kaiwa jiharsa ta Asali, Benue hari inda aka kashe mutane sama da 100.

Karanta Wannan  Hotuna: Jami'an tsaro sun kashe masu garkuwa da mutane 3 a Kaduna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *