
Tsohon Gwamnan jihar Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa irin rikicin da yasa sua bar jam’iyyar NNPP yanzu haka ya mamaye jam’iyyar ADC.
Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na sada zumunta inda yace dan hakane suka fara neman jam’iyyar da zasu sake komawa dan ci gaba da fafutuka.
Yace a yanzu haka suna magana da jam’iyyar NDC da PRP.
Kwankwaso yace kuma maganar fitowa takarar shugaban kasa ko goyon bayan wani dan takarar shugaban kasa duk babu gaskiya a cikinsu.
Sannan yace da ba’a ganshi ba a wasu tarukan jam’iyyar ADC, wani uzuri ne ya hanashi kuma ya sanar da shugabancin jam’iyyar.