
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya nemi kotu ta bashi dama ya je a duba lafiyar idansa da ta hakoransa.
El-Rufai ya nemi hakan ne a gaban babbar kotun jihar Kaduna inda ICPC ta sake gurfanar dashi dan bayyana sabbin tuhume-tuhumen da take masa.
Kotun dai ta amince da wannan bukatar ta malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda tace amma Asibitin da za’a dubashi kada ya wuce Abuja.
Sannan a tabbatar jami’an ICPC zasu bishi.