Sunday, March 16
Shadow

Masu Gàrkùwà da mutane sun sace dalibai 2 a kofar makarantarsu

Rahotanni daga Makurdi Jihar Benue na cewa masu garkuwa da mutane sun sace dalibai biyu daga jami’ar Joseph Sarwuan Tarka University dake jihar.

An yi garkuwa da dalibanne a daren ranar Talata a gaban makarantarsu.

A hirar da aka yi da daya daga cikin daliban me suna Ashar Lubem ya bayyana cewa dalibai 4 ne aka yi garkuwa dasu kuma lamarin ya jefa daliban makarantar cikin rudani.

Kakakin ‘yansandan jihar, Sewuese Anene ta tabbatar da faruwar lamarin saidai tace dalibai 2 ne kadai aka yi garkuwa dasu kamar yanda suka samu bayanai.

tace kuma suna kan binciken lamarin.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Dan takarar gwamnan jihar Edo yana cewa zasu samarwa jihar matsalar tsaro

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *