Tuesday, April 28
Shadow

Masu son zama shugaban kasa sun yi yawa a ADC>>Inji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jigawa, Malam Sule Lamido yace masu son zama shugaban kasa, sun yi yawa a jam’iyyar ADC.

Sule Lamido ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV.

Sule Lamido wanda yana daga cikin wadanda suka halarci taron farko na hadakar ‘yan Adawa da suka zabi APC a matsayin jam’iyyar su, yace ba zai bar PDP zuwa karamar jam’iyya ba.

Yace yana baiwa masu son shugabanci a jam’iyyar ta ADC dasu natsu su zama cewa sun samu alkibla da hafin kai.

Akwai Atiku Abubakar, Peter Obi, Rotimi Amaechi da duka suka bayyana son tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar ta ADC.

Karanta Wannan  Lauyoyin Nnamdi Kanu sun bayyana cewa, basu yadda da Sakamakon gwajin Lafiyar da aka masa ba inda suka ce ko jininsa ba'a dauka ba ta yaya za'a ce yana da lafiyar da zai iya ci gaba da tsayawa a gaban kotu?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *