Friday, May 23
Shadow

Mutumin da ya auri mata 3 a rana daya, yayi bayanin yanda zai gamsar da kowacce daga cikinsu a gado

Mutumin da ya auri mata 3 a rana daya Arube Otor ya bayyana dalilinsa na yin hakan da kuma yanda zai gamsar dasu a gado.

A hirarsa da jaridar Punchng ya bayyana cewa mahaifinsa ma mata da yawa ya aura kuma a gida daya suka zauna ba zaka gane banbanci tsakaninsu ba.

Yace dan haka shima shiyasa yake son yayi gadon mahaifinsa.

Yace dama yana da mata daya kamin auren matan 3 kuma nan gaba yana sonya kara auren guda biyu.

Ya kara da cewa, game da maganar kwana, kowacce zata rika zuwa tana masa kwana 3 a turakarsa har kwanan kowacce ya zagayo.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon tawagar motocin Kakakin majalisa, Sanata Godswill Akpabio da suka dauki hankula

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *