Friday, March 14
Shadow

Nasan cewa matakan dana dauka a mulkina sun saka mutane wahala>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, yasan matakan da gwanatinsa ta dauka na tayar da komadar tattalin arziki sun kawo wahala.

Ya bayyana hakane a jawabin da yayi da safiyar yau na ranar Dimokradiyya.

Inda yace yana sane da wahalar da ‘yan kasa suke sha.

Ya bayyana cewa amma daukar matakan dolene dan dora Najeriya a turba me kyau wadda zata daina dogaro akan man fetur kadai dan samun kudin shiga.

Ya bayyana cewa wannan abu ne da ya kamata a yi shi da dadewa amma shuwagabannin da suka gabata ba su yi ba.

Karanta Wannan  Yau Tsohan Shugaban Kasa Na Mulkin Soja Janar Sani Abacha Ke Cika Shekara 26 Cif Da Rasuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *