Monday, January 19
Shadow

Nasan cewa matakan dana dauka a mulkina sun saka mutane wahala>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, yasan matakan da gwanatinsa ta dauka na tayar da komadar tattalin arziki sun kawo wahala.

Ya bayyana hakane a jawabin da yayi da safiyar yau na ranar Dimokradiyya.

Inda yace yana sane da wahalar da ‘yan kasa suke sha.

Ya bayyana cewa amma daukar matakan dolene dan dora Najeriya a turba me kyau wadda zata daina dogaro akan man fetur kadai dan samun kudin shiga.

Ya bayyana cewa wannan abu ne da ya kamata a yi shi da dadewa amma shuwagabannin da suka gabata ba su yi ba.

Karanta Wannan  Hotunan Yadda Matashiyar Farfesa Aisha Sani Maikudi, Yar Asalin Jihar Katsina Ta Karbi Ragamar Shugabancin Jami'ar Abuja, Yau Litinin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *