
Kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya bayyana cewa ba zai sauka daga kan mukaminsa ba saboda zarge-zargen karya da ake masa.
Ya bayyana hakane bayan da Sanata Natasha Akpoti ke zarginshi da nemanta da lalata sannan kuma Aka zargeshi da aikata magudin zabe.
Akpabio yace idan magana ta shiga kotu aka wankeshi ko wa zai gane cewa shi ba me laifi bane.