Friday, December 5
Shadow

Ni fa nafi damuwa da Tshàgyèràn Dhàjì fiye da mutanen da suke Dàukà>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Malamin addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, yafi damuwa da Tshàgyèràn Dhàjì fiye da mutanen da suke yin Garkuwa da su.

Malam ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace kamar a Asibiti ne idan aka kawo mutum na zubar da jini, ana fara tsayar da jinin ne farko kamin a fara gyaran ciwo ko dinki.

Malam yace misali Mahaukaci ne a kasuwa ya cakawa mutane da yawa wuka, kamata yayi a fara kwace wukar dake hannunsa kamin a fara kula wadanda ya cakawa wukar.

Yace bawai bai damu da wadanda lamarin ‘yan Bindigar ke shafa ba, abinda yake magana akai shine a fara dakatar da zubar da jinin tukunna.

Karanta Wannan  Kwana daya bayan da Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya jinjinawa Gwamnatin Tinubu bisa farfado da tattalin arzikin Najeriya, Bankin Duniya yace duk da kokarin Gwamnati na farfado da tattalin arzikin, Mutane Miliyan 139 ne suka tsunduma cikin bakin Talauci a Najeriya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *