Sunday, March 15
Shadow
Kalli Bidiyon: An jiyo Peter Obi na cewa Musulman Najeriya mabarata ne, kuma bara wani sashe ne na Musulunci

Kalli Bidiyon: An jiyo Peter Obi na cewa Musulman Najeriya mabarata ne, kuma bara wani sashe ne na Musulunci

Duk Labarai
Wani Bidiyon dan takarar shugaban kasa a zaben shakerar 2023 a jam'iyyar Labour Party, Peter Obi ya bayyana inda aka jishi yana cewa Almajiranci da bara na musulmai be Sannan ya alakanta addinin Musulunci da bara Saidai yace Almajirai da suke yawo a tituna zasu iya zama ma'aikata a kamfanoni. Saidai wadannan kalamai sun jawo masa suka sosai a kafafen sadarwa. https://www.tiktok.com/@the_nigerianist/video/7581865063154273554?_t=ZS-927AMNopeoi&_r=1 https://twitter.com/HighChiefOkoro/status/1998776191470227481?t=bi0NiPvyM20SyAUFuDFVNQ&s=19
Shuwagabannin Najeriya ne suka samar da matsalar tsaron da ake fama ita kuma duk randa suka ga dama sune zasu magance ta>>Inji Sheikh Zakzaky

Shuwagabannin Najeriya ne suka samar da matsalar tsaron da ake fama ita kuma duk randa suka ga dama sune zasu magance ta>>Inji Sheikh Zakzaky

Duk Labarai
Malamin Shi'a, Sheikh Ibrahim Zakzaky ya bayyana cewa, Gwamnati ce ta kawo matsalar tsaro Najeriya kuma itace zata magance matsalar idan ta ga dana. Ya bayyana hakane yayin wata Hira da 'yan Jarida suka yi dashi. Yace ta yaya fulani dake daji suna kiwon dabbobi suka samu Bindigu da motocin sulke irin na soji? https://twitter.com/dammiedammie35/status/1998798879412859303?t=MZbwGkuoUg1pK7TjG4C8FA&s=19
Ko a Mafarki ban taba Tunin za’a janye min ‘yansandan dake bani tsaro ba>>Sanata Ningi

Ko a Mafarki ban taba Tunin za’a janye min ‘yansandan dake bani tsaro ba>>Sanata Ningi

Duk Labarai
Sanata Ahmad Ningi ya bayyana cewa, Bai taba Tunanin cewa wata rana za'a wayi gari a janyewa Sanatoci jami'an tsaron 'yansanda dake basu kariya ba. Yace abin takaici shine ga mawaka, 'ya'yan 'yan siyasa, da sauran wadanda basu kamata ba har yanzu 'yansanda na take musu baya. Yace indai an janye musu masu take musu baya, to kamata yayi suma Gwamnoni da Ministoci da shugaban kasa duk a janye musu masu take musu baya. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1998777385500410294?t=BmhI3Cz7YiAIekZI-kHqTA&s=19
Kalli Bidiyon: Nasan Kaina shiyasa na daina daukar Mace a matsayin sakatariya>>Inji Fasto Adeboye

Kalli Bidiyon: Nasan Kaina shiyasa na daina daukar Mace a matsayin sakatariya>>Inji Fasto Adeboye

Duk Labarai
Malamin Kirista Pastor Adeboye ya bayyana cewa, ya daina daukar mace a matsayin sakatariya. Yace dalili kuwa shine lokacin kamin ya samu shiriya, yasan wanene shi. Yace wani lokacin yakan kai har karfe 3 na dare yana aiki, kaga kuwa idan ya dauki sakatariya mace akwai matsala. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1998672355854283193?t=1W093tp_qXTx61yt_IlCug&s=19
Kalli Bidiyon: Naira Dubu dari bakwai nake kashewa idan zan je jihata ta Kebbi daga Abuja>>Inji Sanata Adamu Alero

Kalli Bidiyon: Naira Dubu dari bakwai nake kashewa idan zan je jihata ta Kebbi daga Abuja>>Inji Sanata Adamu Alero

Duk Labarai
Sanata Adamu Aleiro Daga jihar Kebbi ya bayyana cewa tsadar tikitin jirgin sama yayi yawa inda ya kawo misalin cewa daga Abuja zuwa Legas Naira dubu dari biyarne. Yace shima zuwa jiharsa ta Kebbi yakan kashe Naira 700 yake kashewa, zuwa kawai. Yayi kiran a dauki matakin rage farashin tikitin jirgin. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1998689602572349634?t=1O0PDyBD6Yri-knSHfDteQ&s=19
Da Duminsa: Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya shafe kwana na biyu a hannun EFCC

Da Duminsa: Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya shafe kwana na biyu a hannun EFCC

Duk Labarai
Rahotanni daga Abuja na cewa tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami ya shafe kwana na biyu a hannun Hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC. Rahotanni sun ce EFCC ta samu amincewa daga kotu ta ci gaba da tsare tsohon Ministan. Ana zarginsa da laifuka 18 da suka hada da daukar nauyin tà'àddàncy da satar kudade da kuma aikata ba daidai ba da ofishinsa.
Kalli Bidiyon: Yanda Fasto ta Làqàdàwà wani da ta zarga da yi mata sàtà a Choci dùqàn kawo Wùqà

Kalli Bidiyon: Yanda Fasto ta Làqàdàwà wani da ta zarga da yi mata sàtà a Choci dùqàn kawo Wùqà

Duk Labarai
Wannan wata Fastuwace data kama wani data ke zargin yana mata sata a cocinta. An ga yanda ta tara matasa suna dukan wanda suke zargi. Tace tana taimakon sa har ma dansa kyauta yake karatu a makarantarta amma yake mata sata. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1998633946901536801?t=-pTmanvIRuNqTzMTgfzIyg&s=19 Da yawa dai sun ce dukan yayi yawa.