Tuesday, December 16
Shadow
Kalli Bidiyo: Dan Allah duk wanda muka yi fada dashi, dan Darajar wannan dakin ya yafe min>>Inji Hassan Make-Up

Kalli Bidiyo: Dan Allah duk wanda muka yi fada dashi, dan Darajar wannan dakin ya yafe min>>Inji Hassan Make-Up

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Hassan Make-Up ya bayyana cewa, yana neman Afuwar duk wanda suka yi fada dashi ya yafe masa. Ya bayyana hakane yayin da yake kusa da ka'aba yake rokon dan darajar dakin Ka'aban duk wanda suka yi fada dashi ya yafe masa. A baya dai an ga Hassan Make-Up har kuka ya rika yi bayan da ya samu zuwa Aikin Umrah. https://www.tiktok.com/@officielhassanmakeup227/video/7555127311583038776?_t=ZS-90A3JHC3sYq&_r=1
Kalli Bidiyo: Nima ga dana da Kachiya aka Haifeshi, Dan haka, Malam Lawal Triumph yayi daidai, Haihuwar mutum da Kachiya ba Karama bace>>Inji Malam Abdulhamid Dahir

Kalli Bidiyo: Nima ga dana da Kachiya aka Haifeshi, Dan haka, Malam Lawal Triumph yayi daidai, Haihuwar mutum da Kachiya ba Karama bace>>Inji Malam Abdulhamid Dahir

Duk Labarai
Malam Abdulhamid Dahir ya goyi bayan Sheikh Lawal Triumph kan kalaman da yayi cewa, Haihuwar mutum da Kachiya ba karama bane. Malam ya bayar da misali da dansa inda yace shima da Kachiya aka haifeshi dan haka, Haihuwar Mutum da Kachiya ba karama bace. Kalli Bidiyonsa a kasa: https://www.tiktok.com/@sheikh_lawan_triumph/video/7555274342100258055?_t=ZS-90A2h8MjRr7&_r=1
Sanata Ali Ndume ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar rushe kungiyar PENGASSAN

Sanata Ali Ndume ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar rushe kungiyar PENGASSAN

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar rushe kungiyar manyan ma'aikatan man fetur ta PENGASSAN. Yace idan kungiyar ta ci gaba da nuna son kai ba tare da la'akari da abubuwan da zasu kawowa al'umma ci gaba ba, ya kamata Gwamnatin tarayya ta soketa. Ranar Asabat, Kungiyar PENGASSAN ta fara yajin aiki bayan da ta zargi matatar man Dangote da korar membobin ta 800 daga aiki. A bangaren Dangote, yace Wannan yajin aiki PENGASSAN na son yin amfani dashine dan cimma wani buri nata na saka 'yan Najeriya cikin wahala. A hirar da aka yi dashi a Arise TV, Ndume yace baya goyon bayan Ayyukan kungiyoyin kwadago da suke daukar matakan biyan bukatarsu maimakon bukatar al'ummar Najeriya. Yace ina PENGASSAN take a lokacin da aka cire tallafin man fetur a Najeriy...
An tashi baram-baram a zaman sulhu da aka yi yunkurin yi tsakanin kungiyar PENGASSAN da Dangote

An tashi baram-baram a zaman sulhu da aka yi yunkurin yi tsakanin kungiyar PENGASSAN da Dangote

Duk Labarai
Rahotanni sun ce zaman sulhu da aka yi tsakanin wakilan kungiyar PENGASSAN da na Matatar Dangote an tashi ba tare da cimma matsaya ba. Gwamnatin tarayya ce ta kira zaman wanda aka fara ranar Litinin da misalin karfe 4 p.m.. Ministan kwadago, Mohammed Dingyadi da karamar ministan Kwadago, Nkiruka Onyejeocha sun halarci zaman wanda aka shafe awanni 9 ana yi. Minista Dingyadi yace za'a dawo ci gaba da zaman da misalin karfe 2 p.m. na ranar Talata. Gwamnatin tarayya tace tana duba abinda wannan rikici zai jawowa Najeriya ne shiyasa take kokarin sulhunta Bangarorin Dangote da PENGASSAN.
Kalli Bidiyon: An aiko min Sako in daina Karanta Jawahilin Ma’ani>>Inji Malam Lawal Triumph

Kalli Bidiyon: An aiko min Sako in daina Karanta Jawahilin Ma’ani>>Inji Malam Lawal Triumph

Duk Labarai
Bidiyon malam Lawal Triumph inda yake fadin cewa, an aika masa da sako ya daina karanta Jawahiril ma'ani saboda makiya sun yi yawa ya watsu sosai. Malam Lawal Triumph dai a yanzu shine ake ta batunsa a Kano dama kafafen sada zumunta saboda kalaman da basu kamata ba da ake zarginsa da fadi a kan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). https://www.tiktok.com/@sadiq_umar/video/7555431202769980688?_t=ZS-909t5dMQWTQ&_r=1
Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta baiwa membobinta umarnin su shirya shiga yajin aiki dan goyawa Kungiyar PENGASSAN baya a fadan da take da Dangote

Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta baiwa membobinta umarnin su shirya shiga yajin aiki dan goyawa Kungiyar PENGASSAN baya a fadan da take da Dangote

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta yi kira ga Membobinta dasu shirya shiga yajin aiki dan giyawa kungiyar PENGASSAN baya game da fadan da take da matatar man fetur din Dangote. Hakan na zuwane bayan yajin aikin da kungiyar PENGASSAN ta fara wanda ya dakatar da ayyuka a matatar man fetur din Dangote. Kotun Masana'antu ta dakatar da kungiyar PENGASSAN shiga yajin aikin a ranar lit, saidai PENGASSAN tace bata samu hakan a hukumance ba daga kotun. A hirarsa da Punchng, shugaban NLC, Joe Ajaero ya bayyana cewa membobinsu su shirya dan fara yajin aikin nuna goyon baya ba kungiyar PENGASSAN inda ya zargi Matatar man fetur din Dangote da samar da tsare-tsaren masu take hakkokin ma'aikata.
Kwana daya bayan samun Rahoton cewa, zai fito takarar shugaban kasa, Gwamnatin Tarayya ta fara sukar Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan

Kwana daya bayan samun Rahoton cewa, zai fito takarar shugaban kasa, Gwamnatin Tarayya ta fara sukar Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan

Duk Labarai
Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na da ‘yancin tsayawa takarar shugabancin ƙasar a shekarar 2027. Sai dai ta jaddada cewa ‘yan Najeriya ne za su yi masa hukunci saboda ba su manta 'munin' mulkin Jonathan ba, ta kuma kwatanta mulkin Tinubu da abin da ta bayyana a matsayin “gagarumin ci gaban tattalin arziƙi” Fadar shugaban ƙasar ta kuma ɗora alhakin fara yaƙin neman zaɓe da wuri kan masu neman kifar da shugaba mai ci. Hakan na zuwa ne a rana guda da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ba za ta bai wa Jonathan tikitin tsayawa takara kai tsaye ba, inda ta bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin “zaɓuɓɓukan da take dubawa.
Kalli Bidiyon: Kalaman da Sheikh Lawal Triumph ya fadi akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sam basu dace ba, kuma nasan zaku ce ni dan fim ne be kamata in saka baki ba, to Ku sani Annabu aka taba>>Inji Bosho

Kalli Bidiyon: Kalaman da Sheikh Lawal Triumph ya fadi akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sam basu dace ba, kuma nasan zaku ce ni dan fim ne be kamata in saka baki ba, to Ku sani Annabu aka taba>>Inji Bosho

Duk Labarai
Tauraron Fina-finan Hausa a bangaren Barkwanci, Bosho ya yi martani kan zargin da akewa malam Lawal Triumph kan yin kalamai da basu dace ba ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Bosho yace kalaman da Malam Lawal Triumph yayi amfani dasu basu dace ba. Bosho Yace yasan wasu zasu ce a matsayinsa na dan Fim kada ya saka baki amma yace duk wanda ya taba Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko wanene ba zasu bari ba. https://www.tiktok.com/@dr.ishakayahaya/video/7555296755907185928?_t=ZS-909mkB72drV&_r=1
Cikar Najeriya shekara 65 da samun ‘Yanci: Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutu ranar Laraba

Cikar Najeriya shekara 65 da samun ‘Yanci: Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutu ranar Laraba

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta sanar da gobe Laraba a matsayin ranar hutu a ƙasar somin bikin cikar ƙasar shekara 65 da samun ƴancin kai. Cikin wata sanarwa da ministan cikin gida na ƙasar, Olibunmi Tunji-Oja ya fitar, ya taya ƴan Najeriya murnar cimma wannan ''babban matsayi''. Ministan ya kuma buƙaci ƴanƙasar su ci gaba da nuna kishin ƙasa da hadin kai da juriya, waɗanda ya ce su ne ke taimaka wa ƙasar wajen dunƙulewa tun lokacin samun ƴancin kai a 1960. A ranar 1 ga watan Otoban 1960 ne dai Najeriya ta samun ƴancin kai daga Turawan mulkin Birtaniya da suka yi mata mulkin mallaka.