Tuesday, December 16
Shadow
Gwamnati ta bayyana jihohi 11 da zasu fuskanci ambaliyar ruwa tsakanin nan da ranar Alhamis, Karanta ka ji ko jiharka na ciki

Gwamnati ta bayyana jihohi 11 da zasu fuskanci ambaliyar ruwa tsakanin nan da ranar Alhamis, Karanta ka ji ko jiharka na ciki

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta fitar da hasashe na jihohi 11 da ka iya fuskantar ambaliyar ruwa tsakanin ranar Lahadi da ranar Alhamis. Ma'aikatar Muhalli ta tarayya ce ta fitar da wannan sanarwar inda tace jihohin da lamarin zai shafa sun hada da: Adamawa State (Ganye, Natubi); Benue State (Abinsi, Agyo, Gogo, Ito, Makurdi, Udoma, Ukpiam); Nasarawa State (Agima, Rukubi, Odogbo); Taraba State (Beli, Serti, Donga); Delta State (Umugboma, Umukwata, Abraka, Aboh, Okpo-Krika); da Niger State (Rijau). Sauran Jihohin sune Kebbi State (Ribah); Kano State (Gwarzo, Karaye); Katsina State (Jibia); Sokoto State (Makira); da Zamfara State (Kaura Namoda, Shinkafi, Maradun, Gusau, Anka, Bungudu). Saidai mu yi fatan Allah ya tsare.
Ina goyon bayan ciren tallafin man fetur da shugaba Tinubu yayi>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Ina goyon bayan ciren tallafin man fetur da shugaba Tinubu yayi>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Duk Labarai
Me martaba sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya bayyana cewa, yana goyon bayan cire tallafin man fetur da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi. Ya bayyana hakane a wajan wani taron marubuta da aka gayyaceshi. Sarkin Yace Da ba'a cire tallafin Man fetur din ba da Najeriya ta durkushe. Sarki Sanusi na daga cikin na gaba-gaba wajan bayar da shawarar daina biyan tallafin man fetur shekaru da dama da suka gabata.
AbinYa Tabbata: Dangote Ya Tura Motoci 1,000 Masu Amfani Da Gas Don Fara Dakon Man Fetur Kyauta

AbinYa Tabbata: Dangote Ya Tura Motoci 1,000 Masu Amfani Da Gas Don Fara Dakon Man Fetur Kyauta

Duk Labarai
Yau Litinin, manyan motocin dakon man fetur guda 1,000 mallakin kamfanin Dangote, masu amfani da iskar gas (CNG), sun fara aikin dakon man fetur daga matatar man Dangote zuwa gidajen mai a sassan Najeriya kyauta ba tare da caji ba. Wannan mataki na daga cikin kokarin rage tsadar man fetur da kuma karancin da ake fuskanta a wasu yankuna. Ana sa ran hakan zai taimaka wajen kara wadatar man fetur da saukaka farashinsa ga 'yan kasa. Sai dai, a baya irin wannan yunkuri ya fuskanci turjiya daga wasu bangarori, musamman kungiyar direbobi da kuma dillalan man fetur, wadanda ke ganin hakan na iya shafar sana’arsu. Yaya kuke kallon wannan mataki na Dangote ko hakan zai taimaka wajen rage wahalar man fetur a kasar nan, ko kuwa akwai wata barazana da ke tattare da hakan ga masu zaman kansu? ...
Kalli Bidiyo: Maza basu kare ba da mace zata rika neman mace ‘yar Uwarta, idan kika samu maza 10 kika basu Naira Dubu-Dubu da gudu zasu rika zuwa har gida>>Inji Tauraruwar Kannywood

Kalli Bidiyo: Maza basu kare ba da mace zata rika neman mace ‘yar Uwarta, idan kika samu maza 10 kika basu Naira Dubu-Dubu da gudu zasu rika zuwa har gida>>Inji Tauraruwar Kannywood

Duk Labarai
Tauraruwar Kannywood ta bayyana cewa, maza basu kare ba da mace zata rika nema mace 'yar uwarta. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita. Tace idan mace ta samu maza 10 ta basu dubu-dubu har gida zasu rika zuwa. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita. https://www.tiktok.com/@mustaphayalo/video/7549847883604954376?_t=ZS-8zkDdUh9hdB&_r=1
Kalli Bidiyon: Kwanaki 2 bayan kammala dafa shinkafa a Tukunya mafi girma a Duniya, Har yanzu akwai sauran shinkafar bata kare ba

Kalli Bidiyon: Kwanaki 2 bayan kammala dafa shinkafa a Tukunya mafi girma a Duniya, Har yanzu akwai sauran shinkafar bata kare ba

Duk Labarai
Rahotanni sun ce kawanaki 2 bayan kammala dafa shinkafar Hilda Baci wadda ta dafa a Tukunya mafi girma a Duniya, har yanzu akwai sauran shinkafar bata kare ba. Hilda Baci dai ta dafa shinkafa buhu 200 wanda kuma mutane 20,000 suka bayyana son zuwa wajan dan su ci. Saidai duk da haka shinkafar bata kare ba inda a wasu lokutan aka ga Hilda na rokon Mutane su zo su ci shinkafar dan bata san yanda zata yi da ita ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1967215847782670520?t=x--2fHoNqww6bmdclpS0VQ&s=19
Neman Shawara: Zuciyata tana gaya min in shiga Addinin Musulunci, ku bani Shawara>>Inji Moses TheCEO

Neman Shawara: Zuciyata tana gaya min in shiga Addinin Musulunci, ku bani Shawara>>Inji Moses TheCEO

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Moses the CEO ya bayyana cewa, zuciyarsa na gaya masa ya karbi Addinin Musulunci. Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa inda yace yana neman shawarar mutane aka ko ya bi abinda zuciyarsa ke gaya masa ko kuwa a'a? https://www.tiktok.com/@theceo011/video/7548189932834114838?_t=ZS-8zk5358A54r&_r=1 Mosea dai na kawo labaran abubuwan dake faruwa ne a fadin Duniya.
Dangote zai rage farashin man fetur dinsa daga Naira N865 akan kowace lita zuwa Naira N841 a Legas da sauran Jihohin Yarbawa, Sannan A Abuja da jihar Kwara da Edo, ma zai rage farashin man zuwa Naira 851 kan kowace lita

Dangote zai rage farashin man fetur dinsa daga Naira N865 akan kowace lita zuwa Naira N841 a Legas da sauran Jihohin Yarbawa, Sannan A Abuja da jihar Kwara da Edo, ma zai rage farashin man zuwa Naira 851 kan kowace lita

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote zata rage farashin man fetur dinta zuwa daga Naira 865 zuwa Naira 841 akan kowace lita a jihar Legas da sauran Jihohin Yarbawa. Hakanan matatar zata rage farashin kowace lita zuwa Naira 851 a Abuja da kuma jihohin Kwara, da Edo. Hakan na zuwane a yayin da Matatar man ta Dangote ke shirin fara kaiwa gidajen sayar da man fetur man kyauta da motocin tanka na dakon Man fetur din data siyo daga kasashen waje. Rikici tsakanin matatar man fetur ta Dangote da sauran 'yan kasuwar man fetur ya ta'azzara sosai inda suka ce sai ya shiga kungiyarsu amma shi kuma yace hakan ba zata yiyu ba.
Kalli Bidiyo: Wallahi Dan Damusa bai Rasu yana aikata abinda kuke zaagiynsa akai ba>>Inji Me_Rayyan

Kalli Bidiyo: Wallahi Dan Damusa bai Rasu yana aikata abinda kuke zaagiynsa akai ba>>Inji Me_Rayyan

Duk Labarai
Me_Rayyan ya bayyana cewa, Wallahi Dan Damusa bai mutu yana aikata abonda ake zarginsa da aikatawa ba. Yace a lokacin da aka yi sulhu da dan Damusa a Masallaci a Kaduna sun halarci wajan, yace wadanda basu yadda ayi Sulhu ba, Dan Damusa da jami'an tsaro ake zuwa ace su yadda ayi sulhun. https://www.tiktok.com/@me_rayyana/video/7547474386085793031?_t=ZS-8zjxZOdn2iv&_r=1 Rasuwar Dan Damusa dai ta tayar da kura sosai musamman a kafafen sadarwa inda akai ta maganganu da muhawara kala-kala.
Karfin Hali kawai nike ina yin Fim, Yanzu haka ana neman Miliyan 2 dan yimin aikin ciwon zuciya>>Inji Tahir Fage

Karfin Hali kawai nike ina yin Fim, Yanzu haka ana neman Miliyan 2 dan yimin aikin ciwon zuciya>>Inji Tahir Fage

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Tahir Fage ya bayyana cewa, karfin hali yake fina-finan da yake fitowa saboda yana fama da ciwon zuciya Yace ana neman sama da Naira Miliyan 2 dan a masa aiki a Abuja. Ya bayyana hakane a hirar da RFIHausa Suka yi dashi. Ya kuma ce Ko rawar gala da aka ga yayi a kwanakin baya yana neman dubu 250 ne yaran da suka bude gidan galar suka bashi Naira dubu 100 dan ya je a matsayin babban bako. https://www.tiktok.com/@rfi_ha/video/7549833237225278737?_t=ZS-8zjQtmXQvCr&_r=1
Daga yanzu sai limamai sun rika gabatar da Hudubar Juma’a an tantance bata sabawa tsarin Gwamnati ba kamin a amince su hau Munbari su yi ta>>Inji Gwamnan jihar Naija, Umar Bago

Daga yanzu sai limamai sun rika gabatar da Hudubar Juma’a an tantance bata sabawa tsarin Gwamnati ba kamin a amince su hau Munbari su yi ta>>Inji Gwamnan jihar Naija, Umar Bago

Duk Labarai
Gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya bayyana cewa, daga yanzu sai an tantance hudubar Juma'a kamin a yadda limami ya hau Mumbari ya gabatar da ita. Gwamnan ya tabbatar da hakan ne a hirar da aka yi dashi a hidan Talabijin na TVC ranar Lahadi. Yace ba zasu amince da a rika yada hudubar data zama zata cutar da mutane ko gwamnati ba. Gwamnan ya kara da cewa, suna aiki da hukumomin tsaro dan tabbatar da faruwar hakan.