Tuesday, December 16
Shadow
Karanta jadawalin shuwagabannin kasashen Duniya mafiya Arziki

Karanta jadawalin shuwagabannin kasashen Duniya mafiya Arziki

Duk Labarai
Wannan Jadawalin shuwagabannin kasashen Duniya ne mafiya Arziki. Vladimir Putin (Russia) – $258 Bn Donald Trump (United States) – $6.1 Bn Kim Jong Un (North Korea) – $5 Bn Xi Jinping (China) – $1.5 Bn Teodoro Obiang Nguema Mbasogo (Equatorial Guinea) – $940 Mn Ilham Aliyev (Azerbaijan) – $500 Mn Recep Tayyip Erdoğan (Turkey) – $500 Mn Paul Kagame (Rwanda) – $500 Mn Cyril Ramaphosa (South Africa) – $450 Mn William Ruto (Kenya) – $400 Mn
Bayan da wannan hoton nashi ya jawo cece-kuce Gfresh yayi Bidiyo ba Filta inda yace nasu son ganinshi ba Filta gashi

Bayan da wannan hoton nashi ya jawo cece-kuce Gfresh yayi Bidiyo ba Filta inda yace nasu son ganinshi ba Filta gashi

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin yayi Bidiyo ba Filta inda yace masu son ganinshi ba Filta to gashi yayi Bidiyo ba Filta https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7545502116895411463?_t=ZS-8zSMjK3vyfA&_r=1 Hakan na zuwane bayan hotonsa da ya bayyana inda aka ganshi a wajan biki an daukeshu hoto yayi wani iri duk tabo a fuskar.
Da Duminsa: Hukumar ‘yansandan jihar Kaduna ta gayyaci El-Rufai ya gurfana a gabanta dan amsa tambayoyi

Da Duminsa: Hukumar ‘yansandan jihar Kaduna ta gayyaci El-Rufai ya gurfana a gabanta dan amsa tambayoyi

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan jihar Kaduna ta gayyaci tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da wasu 'yan APC 6 su gurfana a gabanta dan amsa tambayoyi. A takardar data fitar yau September 4, 2025 hukumar 'yansandan tace jam'iyyar ADC ta gabatar mata da El-Rufai da wasu mutane 6. Ta zargesu da hannu wajan tunzura mutane da kuma kawo hargitsi a jihar. Sauran wadanda aka gayyata tare da El-Rufai sune Bashir Sa’idu, Jafaru Sani, Ubaidullah Mohammed, Nasiru Maikano, Aminu Abita, da Ahmed Rufa’i Hussaini
2027: Da yiwuwar Kwankwaso ya shiga APC – Kofa

2027: Da yiwuwar Kwankwaso ya shiga APC – Kofa

Duk Labarai
Ɗan majalisar wakilai, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana cewa tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, bai rufe kofar shiga jam’iyyar APC ba gabanin zaɓen 2027. Jibrin, jigo a jam’iyyar NNPP, ya ce Kwankwaso har yanzu ya bar kofar tattaunawa a bude da Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC, duk da kasancewarsa ɗan takarar shugaban kasa a zaɓen 2023. Ya bayyana hakan ne a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels inda ya ƙara da cewa ƙungiyar Kwankwasiyya ƙarfin siyasa ce da ba za a iya watsi da ita ba. Sai dai ya nuna yiwuwar wasu masu ruwa da tsaki a APC na Kano na iya hana shigar Kwankwaso saboda muradunsu na siyasa. Jibrin, wanda ya sha ganawa da Shugaba Tinubu, ya ce komai yana yiwuwa a siyasa, duk da kasancewarsa ɗan Kwankwasiyya. A zaɓen 2023, Kwankwaso ya...
Rundunar yansandan Kano ta kama masu yi mata sojan gona

Rundunar yansandan Kano ta kama masu yi mata sojan gona

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama ƴansandan bogi uku da ake zargi da yin damfara ta hanyar shigar burtu a matsayin ƴansanda a jihar Kano, bayan sun damfari wani mutum naira miliyan ɗaya da dubu talatin. Mutanen da aka kama sun fito ne daga ƙaramar hukumar Daura ta jihar Katsina inda aka kama su a ranar 2 ga Satumba, 2025, a Danagundi Quarters. Rundunar ce ta sanar da hakan a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da Jama’a na ƴansanda, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar. Sanarwar ta ce "Kamar yadda bincike ya nuna, an kama su ne bayan wanda suka damfara ya nemi ɗauki, inda ya yi bayanin yadda abin ya faru. "Binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargi sun yi shigar burtu a matsayin ƴansanda inda suka yi iƙirarin cewa suna da wasu ƙwarewa na musamman da za su t...
Benjamin Hundeyin ya zama kakakin rundunar ƴansandan Najeriya

Benjamin Hundeyin ya zama kakakin rundunar ƴansandan Najeriya

Duk Labarai
Babban Sifeton Ƴansandan Najeriya, Kayode egbetokun ya naɗa CSP Benjamin Hundeyin a matsayin sabon mai magana da yawun rundunar ƴansandan ƙasar (FPRO) Naɗin Hundeyin na ƙunshe cikin wata sanarwa da kakakin rundunar mai barin gado, Muyiwa Adejobi ya fitar. ‎”Babban Sifeton ƴansandan ya buƙace shi da aiki da ƙwarewarsa ta sadarwa wajen inganta aikin ɗansanda a Najeriya ta hanyar ƙarfafa hulda da jama'a,'' in ji sanarwar. Kafin sabon muƙamin, CSP Benjamin Hundeyin ya kasamnce kakain rundunar ƴansanda reshen jihar Legas, inda ya kwashe shekaru yana wannan aiki.
Kalli Bidiyon yanda shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa kasashen Turawa yin hutu

Kalli Bidiyon yanda shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa kasashen Turawa yin hutu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kama hanyar zuwa kasashen Faransa da Ingila inda zai yi hutu acan. Gwamnan Imo dana Legas da sakataren Gwamnatin tarayya na daga cikin wadanda suka mai rakiya zuwa filin jirgin. Fadar shugaban kasa tace shugaban zai kwashe kwanaki 10 ne yana wannan hutun. https://twitter.com/NTANewsNow/status/1963593117988200540?t=gFM_kzD3OO7721pi9xO8VQ&s=19
Kalli Hotuna yanda ‘yansanda suka kulle ofishin Jam’iyyar ADC a jihar Kaduna suka hana jam’iyyar taro

Kalli Hotuna yanda ‘yansanda suka kulle ofishin Jam’iyyar ADC a jihar Kaduna suka hana jam’iyyar taro

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kaduna sun bayyana cewa, 'yansanda sun kulle ofishin jam'iyyar ADC a jihar yayin da kungiyar ke shirin gudanar da taro. Wasu daga cikin 'yan jam'iyyar sun hau kafafen sada zumunta suna bayyana mamaki da rashin jin dadinsu. ""An Jibge Jami'an Tsaro Sama Da Mota 20 Domin A Hanamu Taron Da Zamuyi Ayau" A Ofishin Jami'iyyar ADC Dake Kan Titin Ali Aƙilu. Wacce irin siyasa akeyi haka a jihar Kaduna?, anata amfani da jami’an tsaron da'aka samar domin tsare ƙimar Demokraɗiyya ana yiwa Demokraɗiyyar fyaɗe. sannan a turo wasu wanda basufi ƙarfin cikinsu ba, wanda da ƙyar suke iya biyan kudin haya, suzo media suna kare ƙarya da zalunci. Ance an kashe adawa a jihar Kaduna, to kenan me ake tsoro tunda an kashe adawa?, Allah ya kyauta" Inji Comrades DanHabu ""An Jibge...
Kungiyar Dattawan Arewa ta bukaci shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa ta bukaci shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a Arewa

Duk Labarai
Ƙungiyar dattawan Arewacin Najeriya (NEF) ta buƙaci shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a yankin sakamakon matsalar tsaro da ke ci gaba da ta'azzara wanda ya lalata rayuka da tattalin arzikin ƙasar. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya fitar, ƙungiyar ta bayyana damuwarta kan hare-hare da garkuwa da mutane da kashe su ba ƙaƙautawa da ake ci gaba da yi a yankin. Ya yi gargaɗin cewa idan ba a magance matsalar ba, alummomi ka iya ɗaukar matakin kare kai wanda zai iya kai wa ga ƙazancewar rikicin da kuma kawo cikas ga dimokraɗiyyar ƙasar da zaman lafiyar yankin. "Muna kuma yi kira ga gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai da dama ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci domin ƙara duba girman lamarin, kuma ta aika jam'ian tsaro masu...