Saturday, December 13
Shadow
Kalli Bidiyo: Sunana Sunday Tinubu, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Babana ne, ina neman haduwa dashi ruwa a jallo

Kalli Bidiyo: Sunana Sunday Tinubu, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Babana ne, ina neman haduwa dashi ruwa a jallo

Duk Labarai
Wannan mutumin ya bayyana cewa, sunansa Sunday Tinubu inda yace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu mahaifinsa ne. Yace tun shugaban kasar bashi da komai ya haifeshi. A jawabinsa, yace mahaifiyarsa 'yar rawar Fela ce kuma a haka suka hadu da Tinubu suka haifeshi amma ita ta rasu. https://www.tiktok.com/@cyberopsng/video/7541292483121138952?_t=ZS-8z7DOE1h3ZJ&_r=1
Kalli Bidiyon Tambaya: Rashin Kulawar Mijina yasa na Afkawa Alfasha, Har Ciki ya shiga, menene Mafita?

Kalli Bidiyon Tambaya: Rashin Kulawar Mijina yasa na Afkawa Alfasha, Har Ciki ya shiga, menene Mafita?

Duk Labarai
Wata matar aure ta aikawa da malam Tambayar cewa rashin kulawar da mijinta baya bata tasa ta afka zina . Tace ta gaya masa amma sai yace ta tafi gidansu. Tace bayaj taje gidansu ta yi jini, sai yace ta koma. Tace amma bayan ta koma sai ciki ya shiga kuma ta gano cewa bayan ta yi jinine cikin ya shiga. Tace mijinta yace a zubar da cikin amma ita ta kiya. https://www.tiktok.com/@nuraabunasir/video/7540630374385241351?_t=ZS-8z79hgia69R&_r=1
Yaudarar mu ADC suke, ba zasu iya tsinana komai ba ko da sun samu mulki>>Inji Datti Baba Ahmad

Yaudarar mu ADC suke, ba zasu iya tsinana komai ba ko da sun samu mulki>>Inji Datti Baba Ahmad

Duk Labarai
Tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar ADC, Datti Baba Ahmad ya bayyana cewa, Jam'iyyar ADC yaudarar talakawa kawai suke ko sun samu mulki babu wani ci gaba da zasu iya kawowa. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV ranar Juma'a. Datti na wannan maganar ne duk da cewa, Peter Obi wanda suka yi takara tare a yanzu yana jam'iyyar ADC. Datti dai yace, yana fatan Peter Obi zai koma jam'iyyar Labour party yayi takara acan. Da aka tambayeshi ko zai sake yiwa Peter Obi takarar mataimakin shugaban kasa? Datti Baba Ahmad ya ce Eh.
Usman da Umar (AS) zasu iya canja hukuncin da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi kuma hakan yayi daidai>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Usman da Umar (AS) zasu iya canja hukuncin da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi kuma hakan yayi daidai>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Duk Labarai
Babba Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, Sahabban Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Umar da Usman (AS) zasu iya canja hukuncin sa Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) yayi kuma hakan yayi daidai. Yace Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya basu wannan matsayi na cewa, duk hukuncin da suka yi ya zama shari'a. Malam ya bayyana hakane a wajan karatun da yake ranar Juma'a a masallacin Sultan Bello dake Kaduna a ranar 22/8/2025. Wakilin hutudole ya halarci wajan karatun inda malam yayi wannan maganane a yayin da yake bayar da misalin ikirarin 'yan shi'a na cewa, Khalifanci Aliyu (AS) ne ya kamata a baiwa kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya bar wasiyya kan hakan. Malam yace ko da ace Annabi(Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya bar wasiyya akan hakan am...
Kalli Bidiyo: Yanzu mun gano cewa Tinubu baya kishin Addini, Baya sauraren mu, Muna fatan Allah ya saukeshi karya kara shekara daya akan Mulki>>Inji Malaman da suka tallata Tinubu a 2023

Kalli Bidiyo: Yanzu mun gano cewa Tinubu baya kishin Addini, Baya sauraren mu, Muna fatan Allah ya saukeshi karya kara shekara daya akan Mulki>>Inji Malaman da suka tallata Tinubu a 2023

Duk Labarai
Daya daga cikin malaman da suka tallata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2023 ya fito ya bayyana cewa a yanzu basu tare da shugaban kasar. Yace sun yiwa shugaban kasar kamfe da zuciya daya dan ci gaban Addini, amma sun gano cewa, ba ci gaban addinine a gabansa ba. Yace dan haka suna rokon Allah kamar yanda ya dorashi mulki Allah a saukeshi: https://www.tiktok.com/@yusufautalazio1/video/7539794814984850696?_t=ZS-8z6xC7WQYNc&_r=1
Yayin da Gwamnati ke shirin cire tallafin wutar Lantarki, Kungiyar Kwadago tace hakan zai kara jefa mutane da yawa cikin Talauci

Yayin da Gwamnati ke shirin cire tallafin wutar Lantarki, Kungiyar Kwadago tace hakan zai kara jefa mutane da yawa cikin Talauci

Duk Labarai
Kungiyar kwadago ta NLC tace shirin gwamnati na cire tallafin wutar Lantarki zai jefa dubban 'yan Najeriya cikin wahalar rayuwa, sannan zai durkusar da kasuwanci da yawa da yanzu haka suke fama. Sakataren riko na kungiyar, Comrade Benson Upah ne ya bayyana hakan inda yace cire tallafin, zai karawa rayuwa tsada a Najeriya. A baya dai Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya tabbatar da cewa, Gwamnati zata cire tallafin wutar saboda 'yan Najeriya su rika biyan ainahin kudin wutar da suke sha. Saidai bayan cire tallafin man fetur hakannya jefa mutane da yawa cikin wahalar rayuwa.
Duk me tunanin Tinubu ba zai sake cin zabeba a 2027 mahaukaci ne lamba 1>>Inji Farfesa Haruna Yarima

Duk me tunanin Tinubu ba zai sake cin zabeba a 2027 mahaukaci ne lamba 1>>Inji Farfesa Haruna Yarima

Duk Labarai
Farfesa Haruna Yarima wanda tsohon dan majalisar tarayya ne ya bayyana cewa, duk me tunanin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai sake cin zabe a shekarar 2027 ba mahaukaci ne. Yayi fadi hakane a martaninsa ga masu cewa, Tinubu idan bai sauke Kashim Shettima a matsayin mataimaki ba ya dauko wani musamman Kirista ba zai ci zaben 2027 ba. Farfesa Yerima ya bayyana cewa, wannan magana ba gaskiya bane domin kuwa kamin shugaba Tinubu ya dauko Kashim Shettima a matsayin mataimaki, saida ya lura da abubuwa da yawa. Yace dan haka a yanzu ko da wani zai kawo maganar a canja Kashim Shettima a matsayin mataimaki, Shugaba Tinubu ne da kansa zai fara cewa bai yadda ba.