Saturday, December 13
Shadow
Tinubu ya bar Japan zuwa ƙasar Brazil zai kuma yada zango a Los Angeles – Fadar shugaban ƙasa

Tinubu ya bar Japan zuwa ƙasar Brazil zai kuma yada zango a Los Angeles – Fadar shugaban ƙasa

Duk Labarai
Tinubu ya bar Japan zuwa ƙasar Brazil zai kuma yada zango a Los Angeles - Fadar shugaban ƙasa Fadar shugaban ƙasa ta ce shugaba Bola Tinubu ya zarce Brazil bayan halartar taruka a Japan. A wata sanarwa da kakakin shugaban kasa, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu zai hada zango a birnin Los Angeles na kasar Amurka kafin ya wuce birnin Brasilia na kasar Brazil domin ziyarar aiki da zai fara daga ranar 24 ga watan Agusta.
Rundunar sojin Najeriya ta ce kiran kare kai ba ya nufin mallakar makami

Rundunar sojin Najeriya ta ce kiran kare kai ba ya nufin mallakar makami

Duk Labarai
Shalkwatar tsaron Najeriya ta yi ƙarin haske kan kalaman da babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya yi kan batun kare kai daga hare-haren ƴan fashin daji. Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ta fitar ta ce kalaman Janar Musa ba suna ƙarfafa wa mutane mallakar makami ba ne, kamar yadda wasu kafofin labarai a ƙasar ke yaɗawa. ''Abin da yake nufi shi ne ƴan ƙasa su koyi dabarun kare kai da duniya ta amince da su kamar ƙwarewar tuƙi, da judo da ninƙaya da dambe ko kokawa da sauransu'', in ji sanarwar. ''Kalamansa ba sa nufin mallakar makami ta haramtacciyar hanya, saboda yana sane da dokokin Najeriya da suka haramta mallakar makami''. A ranar Alhamis ne cikin wata hira da gidan Talbijin an Channels, Janar Musa ya ce ya kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarun...
Lokaci yayi da zaku fara kare kanku>>Shugaban Sojojin Najeriya ya baiwa ‘yan Najeriya shawara

Lokaci yayi da zaku fara kare kanku>>Shugaban Sojojin Najeriya ya baiwa ‘yan Najeriya shawara

Duk Labarai
Babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Musa ya shawaraci ƴan Najeriya da su laƙanci dabarun kare kai daga haɗurra a matsayin mataki na ko-ta-kwana. C.G Musa ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels a yau Alhamis. Matsalar tsaro na addabar yankuna da dama na Najeriya, inda masu ɗauke da makamai ke kashe mutane tare da tarwatsa su daga muhallansu. Duk da cewa hukumomi na cewa suna bakin ƙoƙarinsu, amma lamarin na ci gaba da laƙume ɗaruruwan rayuka a yankunan da ake fama da irin waɗannan tashin-tashina, kamar arewa maso yamma da arewa maso gabas da kuma arewa ta tsakiyar ƙasar. Lokacin da aka tambayi Christopher Musa kan ko ya kamata al'umma su koyi dabarun faɗa, ya ce "Ya kamata mutane su ɗauki wannan tamkar koyon tuƙi ne ko iyo, wannan abu...
Ji Yanda Dan gidan Peter Obi yayi martani kan zargin da ake masa cewa, shi dan Lùwàdì ne

Ji Yanda Dan gidan Peter Obi yayi martani kan zargin da ake masa cewa, shi dan Lùwàdì ne

Duk Labarai
Dan gidan Peter Obi, Oseloka Obi yayi martani kan zargin da ake masa cewa shi dan luwadi ne. Hotuna da yawa sun watsu a kafafen sada zumunta inda ake bayyana cewa, Oseloka Obi dan Luwadi ne. Saidai a martanin da yayi a kafar sadarwarsa yace shi ba dan Luwadi bane kawai ana masa wannan kazafi ne saboda mahaifinsa dan siyasa ne. Hotunan Oseloka Obi da wani da ake cewa Na miji ne da ya canja halittarsa zuwa mace sun watsu inda ake zargin suna luwadi ne. Saidai Oseloka Obi yace duk karyane.
Kalli Bidiyon: Diyar tsohon Gwamnan Kano, Balaraba Ganduje ta bayar da Naira Miliyan 10 a wajan bude shagon kwalliya na Tauraruwar fina-finan Hausa Rashida Mai Sa’a

Kalli Bidiyon: Diyar tsohon Gwamnan Kano, Balaraba Ganduje ta bayar da Naira Miliyan 10 a wajan bude shagon kwalliya na Tauraruwar fina-finan Hausa Rashida Mai Sa’a

Duk Labarai
Diyar tsohon gwamnan Kano, Hajiya Balaraba Ganduje, ta bayar da gudummawar Naira Miliyan 10 a wajan bude shagon kwalliya na Tauraruwar fina-finan Hausa, Rashida Mai sa'a. An ga Hajiya Balaba na bayyana hakane a cikin sabon shagon na Rashida Mai Sa'a. https://www.tiktok.com/@sardunan_matasan_gwoza/video/7541067415883353351?_t=ZS-8z5Z0D4RgsC&_r=1
Dole Tinubu ya dauki mataimaki Kirista ko kuma ya fadi zabe a 2027>>Inji Wata Kungiyar Kirista

Dole Tinubu ya dauki mataimaki Kirista ko kuma ya fadi zabe a 2027>>Inji Wata Kungiyar Kirista

Duk Labarai
Wata kungiya me suna Northern Ethnic Nationality Forum ta yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu barazanar faduwa zabe muddin bai daiki mataimaki Kirista ba. Kungiyar ta bakin shugabanta,Dominic Alancha ta jawo hankalin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da cewa, kada ya maimaita kuskuren sake zabar Muslimi a matsayin abokin takararsa a 2027. Alancha yace dolene Tinubu ya dauki mataimaki Kirista daga daya daga cikin jihohin Plateau, Benue, ko Taraba dan kaucewa tunanin da akewa gwamnatinsa na son mayar da Najeriya kasar Musulmi. Sun yi gargadin cewa, sakw daukar musulmi a matsayin mataimaki, zai sa 'yan Adawa su yi nasara.
Buhari ba mutum bane irin mu, wani na musamman ne daga Allah ya zo da siffar mutane>>Inji Bisi Akande

Buhari ba mutum bane irin mu, wani na musamman ne daga Allah ya zo da siffar mutane>>Inji Bisi Akande

Duk Labarai
Buhari wani Mala'ika ne da ya zo a siffar mutane - Akande Chief Bisi Akande mai mallakin jam'iyyar APC Kuma tsohon Gwamnan Jihar Osun ya yi ta'aziyyar rasuwar marigayi tsohon shugaban ƙasar Najeriya Muhammad Buhari, inda ya ayyana shi a matsayin wani Mala'ika ne da ya zo da jikin mutum, wanda ya bar tarihi a Najeriya. Akande ya jagoranci tawagar manyan ƴan siyasa zuwa Kaduna domin yin ta'aziyya ga iyalan sa, yana mai bayyana damuwa ga rasuwar tsohon shugaban ƙasar. Da yake bayyana ganin shi na ƙarshe na tsohon shugaban ƙasar a Daura, Bisi Akande ya gansa da lafiyar sa da ƙwarin sa, wanda ya nuna babu wata alamar rashin lafiya, wanda ya nuna mutuwa dole ce ga kowa.
Shugaban Sojojin Najeriya ya bayyana masu daukar nauyin matsalar tsaro da abinda suke son cimmawa a Najeriya

Shugaban Sojojin Najeriya ya bayyana masu daukar nauyin matsalar tsaro da abinda suke son cimmawa a Najeriya

Duk Labarai
Shugaban hedikwatar tsaro ta kasa, Christopher Musa ya zargi cewa, yawaitar matsalar tsaron da ake fama da ita a Najeriya na da alaka da gabatowar zaben 2027. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Yace idan ba haka ba, ta yaya, shekarar data gabata an samu rahoton raguwar matsalar tsaro sosai amma a wannan shekarar abubuwa su kara dagulewa? Yace 'yan siyasa ne ke daukar nauyin 'yan Bindigar inda ya kara dacewa abinda suke son cimma shine bata sunan Gwamnati ace bata kokari. Yace amma abin takaici shine ta yaya zaka rika kashe mutanen da kake son mulka? Ya kuma zargi cewa, bayan masu daukar nauyin 'yan Bindigar a cikin gida, akwai kuma masu daukar nauyin 'yan Bindigar daga kasashen waje.