Sunday, July 13
Shadow
Son kai irin na Atiku ne yasa na kusa dashi sai kama gabansu suke suna barinshi>>Wike

Son kai irin na Atiku ne yasa na kusa dashi sai kama gabansu suke suna barinshi>>Wike

Duk Labarai
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa, son kai irin na Atiku Abubakar ne yasa mutanen dake kewaye dashi suke watsewa suna barinshi. Ya bayuana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Lere Olayinka. Wike ya bayar da misalin Ifeanyi Okowa wanda yawa Atiku takarar mataimakin shugaban kasa a zaben 2023 amma yanzu ya koma APC. Sannan Akwai Gbenga Daniel, wanda shine daraktan yakin neman zaben Atiku a shekarar 2019 amma shima ya bar PDP, Hakanan kuma yace akwai su Udom Emmanuel Umo Eno wanda duk suke nesanta kansu da jam'iyyar PDP. Wike yace son kaine irin na Atiku ya jawo hakan.
Kalli Bidiyo: A karin farko tun bayan da aka daura aurensu da A’isha Humaira, Rarara yayi magana

Kalli Bidiyo: A karin farko tun bayan da aka daura aurensu da A’isha Humaira, Rarara yayi magana

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tauraron mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ya saki wata sabuwar waka a shafinsa na sada zumunta, karin farko tun bayan daura aurensa da A'isha Humaira. https://www.tiktok.com/@kahuturarara/video/7499222441986657591?_t=ZM-8vz5iH8ce2w&_r=1 Tun bayan da aka daura aurensu a Maiduguri ba'a sake jin duriyar Rarara ba sai da ya saki wannan waka.
Kalli Bidiyo: Gobara a rumbun adana makamai a barikin soji na Giwa da ke Maiduguri ta haifar da fargaba a birnin inda makamai sukai ta fashewa mutane na ta gudun ceton rai

Kalli Bidiyo: Gobara a rumbun adana makamai a barikin soji na Giwa da ke Maiduguri ta haifar da fargaba a birnin inda makamai sukai ta fashewa mutane na ta gudun ceton rai

Duk Labarai
Gobara a rumbun adana makamai a barikin soji na Giwa da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya ta haifar da fargaba a birnin. Ƙarar abubuwa masu fashewa da aka ji a kwaryar Maiduguri sakamakon gobarar cikin dare da aka samu a barikin ya tada hankali, inda wasu rohotanni ke cewa harin Boko Haram ne. https://www.tiktok.com/@officialmannass1/video/7499254467380923653?_t=ZM-8vz4ui4NqsQ&_r=1 To sai dai tuni mataimakin gwamnan jihar Borno Dakta Umar Usman Kadafur ya bukaci mazauna birnin da su kwantar da hankulansu tare da kasance cikin gidajensu, yayin da jami'an tsaro da ƴan kwana kwana ke aikinsu, sakamakon gobarar da ya tabbatar da aukuwar ta. https://www.tiktok.com/@ali.tallafi/video/7499253158410063109?_t=ZM-8vz5Sx2vV4Q&_r=1 htt...
Shin wai me yasa ‘yan kudu suke ta fitowa suna nuna Tinubu suke son ya zama shugaban kasa a 2027 wasu ma har cewa suke basu son dan Arewa amma babu wani babba a Arewa dake mayar da martani?

Shin wai me yasa ‘yan kudu suke ta fitowa suna nuna Tinubu suke son ya zama shugaban kasa a 2027 wasu ma har cewa suke basu son dan Arewa amma babu wani babba a Arewa dake mayar da martani?

Duk Labarai
A 'yan Kwanakinnan mutane da yawa daga yankin kudancin Najeriya sai fitowa suke suna nuna goyon bayansu ga shirin zarcewar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027. Da ga ciki ma wasu na nuna basa son dan Arewa. Na bayabayannan shine wanda Tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a PDP a shekarar 2023, Ifeanyi Okowa ya fada bayan komawarsa APC. Karara ya fito yace mutanensa dan Arewa ne basa son zaba shiyasa ma bai kawo jiharsa ta Delta ba a wancan karin, yace yana sane ya ki bin abinda mutanensa ke so na ya goyi bayan dan kudu, inda yace a yanzu yayi dana sani. Sai kuma maganar da ake alakantata da Ministan Abuja, Nyesom Wike inda aka ruwaito yace nan da shekarar 2027 yunwar da zata kama 'yan Arewa da kansu zasu rika rokon a basu dubu 2 su zabi APC. Duk da ...
Ya kamata mutane su shiga taitayinsu su daina yada karya da bata sunan dan shugaban kasa, Seyi Tinubu>>Kungiyar Kiristoci ta CAN ta yi gargadi

Ya kamata mutane su shiga taitayinsu su daina yada karya da bata sunan dan shugaban kasa, Seyi Tinubu>>Kungiyar Kiristoci ta CAN ta yi gargadi

Duk Labarai
Kungiyar Kiristoci ta CAN reshen Jihohin Arewa 19 da Abuja ta bayyana rashin jin dadinta kan yanda ake samun wasu suna batawa dan shugaban kasa, Seyi Tinubu suna da yada karya akansa. Shugaban kungiyar, John Joseph Hayab ne ya bayyana hakan inda yace mutane su sani akwai rayuwa bayan mahaifinsa, Tinubu ya sauka daga shugaban kasa. Ya kara da cewa, yada karya ya sabawa Al'ada da Addinin da muke bi. Yace dan haka kamata yayi kafafen watsa labarai su rika tantance labari kamin su yadashi.
Gwamnan jihar Rivers da Tinubu ya dakatar, Fubara ya je gidan Wike dan neman a sasanta, ji yanda ya kwanta kasa yana rokon Wike

Gwamnan jihar Rivers da Tinubu ya dakatar, Fubara ya je gidan Wike dan neman a sasanta, ji yanda ya kwanta kasa yana rokon Wike

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, dakataccen gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara ya je gidan ministan Abuja, Nyesome Wike dan neman a sasanta. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da Fubara ya gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a birnin Landan. Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun da tsohon gwamnan jihar, Olusegun Osoba ne suka yiwa Fubara jagoranci zuwa gidan Wike. Rahoton yace Fubara ya kwanta kasa ya gaishe da Wike inda ya rika kiransa da Ogana Ogana. Wata majiya tace sai can duhu yayi sosai sannan Fubara ya bar gidan. Hakanan majiyar ta kara da cewa, Wike ya bukaci Fubara ya je ya tara mutanensa ya gaya musu ainahin abinda ya hadasu fada. Kakakin Wike, Lere Olayinka ya tabbatar da faruwar lamarin amma bai bayar da cikakken bayanin abinda ya faru ba
‘Yan Najeriya 203 da suka maƙale a Libya sun koma gida

‘Yan Najeriya 203 da suka maƙale a Libya sun koma gida

Duk Labarai
Hukumar agajin gaggawa a Najeriya ta ce ta karɓi 'yan ƙasar 203 da aka kwaso daga Libya bayan sun kasa fitowa daga ƙasar ta arewacin Afirka. Jim kaɗan bayan isarsu filin jirgin sama na Murtala Muhammed a Legas a jiya Litinin ne jami'an hukumar ta tarɓe su. Jirgin kamfanin Al Buraq ne ya kwaso mutanen, waɗanda suka ƙunshi maza manya 50, mata manya 96, da yara 29, da kuma jarirai 28. Ƙungiyar kula da ƙaura ta duniya wato International Organisation for Migration (IOM) ce ta ɗauki nauyin mayar da su gida bisa haɗin gwiwa da hukumar National Emergency Management Agency (Nema) da sauran hukumomi. Wata sanarwa da Nema ta fitar ranar Talata ta ce biyu daga cikin mutanen na buƙatar kulawar gaggawa, "kuma nan take aka kai su asibitin Ikeja domin duba su".
Shaguna kusan 500 ne suka ƙone a kasuwar Terminus ta Jos

Shaguna kusan 500 ne suka ƙone a kasuwar Terminus ta Jos

Duk Labarai
Shaguna kusan 500 ne suka ƙone ƙurmus sanadin tashin gobara a babbar kasuwar Jos da aka fi sani da Terminus a jihar Filato ta tsakiyar Najeriya. Yankasuwar sun ce gobarar ta tashi ne da tsakar daren jiya Talata kuma sun yi asarar dukiya ta miliyoyin naira. Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta ce mutum 309 ne shuganansu suka ƙone tare da kayan ciki, sai wasu 58 da 'yandaba suka wawashe. Mustapha Ibrahim Bako, shi ne shugaban kasuwar ta Terminus kuma ya faɗa wa BBC cewa rashin zuwan motocin kashe gobara da wuri ne ya jawo ta'azzarar ɓarnar. "Halin da ake ciki babu daɗi, a jiya mun kwashe mutane sun fi 10 saboda hayaƙin da suka shaƙa, wasu kuma firgici," in ji shi. Ya nemi gwamnatin jihar da "kada ta ce za ta kori kowa a kasuwar, saboda akwai wuraren da wutar ba ta shafa ...