Sunday, March 1
Shadow
Ana ta surutu wai muna hada maza da mata a wajan Maulidi, to ba zamu daina hada maza da mata a wajan maulidi ba>>Inji Anisee

Ana ta surutu wai muna hada maza da mata a wajan Maulidi, to ba zamu daina hada maza da mata a wajan maulidi ba>>Inji Anisee

Duk Labarai
Shahararren dan darika, Masoyin Shehu Tijjani Alhaji Anisee ya bayyana cewa, ba zasu daina hada maza da mata a wajan Maulidi ba Ya bayyana hakane a matsayin raddi ga wani malamin darika da yace saboda hada maza da mata a wajan Maulidi ya kamata a daina yinsa. Saidai Anisee yace a ko inama ana hada maza da mata dan haka su ma a wajan Maulidi ba zasu daina ba.
Faduwar Farashin Abinci: Baku ga komai ba, nan gaba farashin zai kara faduwa sosai kuma gidan kowa sai ya wadata>>Iniji Gwamnatin Tinubu

Faduwar Farashin Abinci: Baku ga komai ba, nan gaba farashin zai kara faduwa sosai kuma gidan kowa sai ya wadata>>Iniji Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya tace 'yan Najeriya basu ga komai ba game da faduwar farashin Abinci da aa gani. Hakan na zuwa ne bayan da hukumar kididdiga ta NBS ta tabbatar da cewa, farashin kayan masarufi yayi ksa a Najeriya inda a yanzu makin bai wuce 20 ba. A yayin hira da manema labarai, me baiwa shugaban kasa shawara akan tattalin arziki, Tope Fasua yace abincin zai sake karyewa sai ya koma kasa da maki 10. Hakan na zuwane yayin da manoma a Arewa ke kokawa da cewa, sune ake hari wannan karya farashin abincin da ake.
Kalli Bidiyo: Akwai wadanda suka fini kudi a Najeriya>>Inji Dangote

Kalli Bidiyo: Akwai wadanda suka fini kudi a Najeriya>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa akwai wanda suka fishi tsabar kudi a Nijeriya. Yace amma basu saka kansu cikin irin rigimar da ya saka kanshi ba. Yana magana ne kan gina matatar man fetur dinsa da kuma rikicin da ya kunno kai tsakaninsa da kungiyar NUPENG. Dangote yace amma dole ne sai an tallafawa gwamnati, yace ba komai ne za'a nade hannu ace wai gwamnati ce zata yi ba. Yace akwai abubuwan da dole sai mutane masu zaman kansu sun saka hannu, yace amma irin abinda ake masa zai sa mutane su guji zuwa zuba hannun jari a Najeriya. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1967987170138079720?t=jK8EwhBa8X1in8Zo76GyHQ&s=19
Yayinnda manoma ke Korafi: Farashin kayan abinci ya sade faduwa kasa

Yayinnda manoma ke Korafi: Farashin kayan abinci ya sade faduwa kasa

Duk Labarai
Hukumar ƙididdiga ta Naajeriya, NBS, ta ce farashin kayayyaki ya faɗo karo na biyar a jere a ƙasar, a watan Agusta 2025, lamarin da ya kawo sauƙi ga mutanen ƙasar. Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna cewa, farashi ya sauko daga 21.88 a watan Yuli zuwa 20.12 a watan Agustan 2025. Abin da ke nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 cikin ɗari daga watan na Yuli zuwa Agusta. Hakan kuma na nufin farashin ya rikito idan aka kwatanta da 32.15 ciki ɗari da aka samu a watan Agustan 2024. Sai dai alƙaluman ba su yi wani tasiri na azo-a-gani ba a yankunan karkara, inda kuɗin mota da rarraba kayayyaki ke ci gaba da janyo tsadar kayayyaki fiye da a birane. Sai dai abinci, wanda shi ne ja gaba wurin kayayyakin da farashinsu ke ƙaruwa ya dawo matsakaici a watan na Agusta a ƙasar, ko da yake y...
Albashin da nake biyan Direbobin Tankana ya fi na wanda ya kammala jami’a>>Inji Dangote

Albashin da nake biyan Direbobin Tankana ya fi na wanda ya kammala jami’a>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa, Albashin da yake biyan direbobin Tankarsa ya fi na wanda ya kammala jami'a. Dangote ya bayyana hakane a wata ganawa da yayi da manema labarai inda yayi karin haske kan rikicinsa da Kungiyar NUPENG. Ya kuma gayyaci direbobin NUPENG duk wanda bai da aiki ya je zai bashi aikin tukin. Dangote yace Albashin Direban tankarsa ya nunka mafi karancin Albashin sau 4 wanda akalla zai kai sama da Naira dubu dari uku kenan.

DSS ta maka Sowore da X da Facebook a kotu saboda ya kira shugaba Tinubu me laifi kuma ya zargi shugaban kasar da fadar ba daidai ba game da magance matsalar rashawa da cin hanci a Najeriya

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS ta maka mawallafin jaridar Sahara reporters, Omoyele Sowore a kotu bisa zarginsa da kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu me laifi. Sannan an zargi Sowore da kuma bayyana shugaban kasar a matsayin makaryaci saboda yace yayi ikirarin magance matsalar rashawa da cin hanci a kasar Brazil amma Sowore yace maganar ba gaskiya bace. Sowore ya wallafa cewa DSS na shirin kaishi kotu kuma a shirye yake idan an kaishi Kotun ya ansa gayyata.
Babu Yunwa a Najeriya>>Inji Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga

Babu Yunwa a Najeriya>>Inji Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga

Duk Labarai
Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya musanta ikirarin tsohon Mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar cewa akwai yunwa a Najeriya. Atiku yace yunwar dake Najeriya da Talauci ka iya tunzura mutane su fita zanga-zanga irin wadda ake yi a kasashen Duniya. Saidai me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya musanta maganar ta Atiku inda yace Atiku be san halin da Najeriya take ciki ba a yanzu dan an kama hanyar ci gaba. Yace Hukumar kididdiga ta kasa, NBS ta fitar da bayanai cewa farashin kayan masarufi sun yi kasa, sannan a baya tace kudaden shigar Najeriya sun karu ta bangaren da ba na man fetur ba. Sannan yace Tinubu ya biya basuka da yawa da ake bin Najeriya. Yace kuma Tinubu ya dauki matakai na gyara kasa ba tare da tsoro ba.