Thursday, March 5
Shadow
Ji irin rawar da mahaifiyar RUKAYYA MUHAMMAD FEMA ta taka wajan nasarar data samu a wajan Muqabala ta Duniya

Ji irin rawar da mahaifiyar RUKAYYA MUHAMMAD FEMA ta taka wajan nasarar data samu a wajan Muqabala ta Duniya

Duk Labarai
Yadda Mahaifiyar Gwarzuwar Muƙabala Ta Duniya Ta Shiga Cikin Tarihi. Hajiya Fatima Umar Mairiga, mahaifiyar gwarzuwar muƙabala ta duniya, RUKAYYA MUHAMMAD FEMA, ta taka gagarumar rawa wajen tabbatar da nasarar diyar ta tun tana ƙarama. Hajiya Fatima ba wai kawai ta tsayu wajen tarbiyya da karfafa gwiwa ba, har ma ta rungumi addu’a a matsayin hanya mafi muhimmanci wajen ganin ɗiyarta ta cimma nasara a rayuwa. Tun tana ƙarama, Rukayya da mahaifiyarta ke tashi cikin dare domin gabatar da Sallar Tahajjud, suna roƙon Allah ya azurta ta da ilimi mai amfani, hikima, da fasaha. Wannan kyakkyawar alaka da Allah da kuma tsantsar jajircewa ya kasance ginshikin nasarar da ta samu. A cikin gagarumar gasa ta duniya – TeenEagle Global Finals 2025 da aka gudanar a birnin London, ƙasar Ingila,...
Shugaba Tinubu Ya Taya Dalibai Uku ‘Yan Arewa Murna Bisa Nasarar Da Suka Samu A Gasar Turanci Ta Duniya (TeenEagle)

Shugaba Tinubu Ya Taya Dalibai Uku ‘Yan Arewa Murna Bisa Nasarar Da Suka Samu A Gasar Turanci Ta Duniya (TeenEagle)

Duk Labarai
Shugaba Tinubu Ya Taya Dalibai Uku ‘Yan Arewa Murna Bisa Nasarar Da Suka Samu A Gasar Turanci Ta Duniya (TeenEagle). Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Nafisa Abdullahi Aminu mai shekaru 17, Rukayya Muhammad Fema mai shekaru 15, da Hadiza Kashim Kalli murna bisa nasarar da suka samu a gasar TeenEagle ta duniya da aka gudanar a birnin London, Ƙasar Ingila. Nafisa ce ta lashe kyautar gwarzon daliba a fannin ƙwarewar harshen Turanci, yayin da Rukayya ta zama ta farko a muhawara, Hadiza kuma ta samu kyautar zinariya a matsayin mai hazaka. Shugaba Tinubu ya jinjinawa waɗannan matasa na Najeriya da suka ɗaga tutar ƙasa a idon duniya, yana mai cewa wannan nasara alama ce ta hasken makomar ƙasar. Ya kuma yaba da irin gudunmawar cibiyoyin ilimi da gwamnatocin jihohi wajen haɓaka ƙwar...
Wannan Bidiyon na Rayya da aka ganta a wani yanayi ya dauki hankula

Wannan Bidiyon na Rayya da aka ganta a wani yanayi ya dauki hankula

Duk Labarai
Bidiyon tauraruwar fina-finan Hausa, Rayya da ya bayyana inda aka ganta sanye da kaya ba dankwali ya dauki hankula a kafafen sadarwa. Wasu dai saboda irin yanda ta bayyana a Bidiyon suna cewa ba ita bace. https://www.tiktok.com/@rayya.official4/video/7533739372231871750?_t=ZS-8yeEUFc4Nur&_r=1 Menene ra'ayinku akai? https://www.tiktok.com/@danmutum.1/video/7535128825768824070?_t=ZS-8yeGBLnRof3&_r=1
Masu son zama shugaban kasa sun yi yawa a ADC>>Inji Sule Lamido

Masu son zama shugaban kasa sun yi yawa a ADC>>Inji Sule Lamido

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Jigawa, Malam Sule Lamido yace masu son zama shugaban kasa, sun yi yawa a jam'iyyar ADC. Sule Lamido ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Sule Lamido wanda yana daga cikin wadanda suka halarci taron farko na hadakar 'yan Adawa da suka zabi APC a matsayin jam'iyyar su, yace ba zai bar PDP zuwa karamar jam'iyya ba. Yace yana baiwa masu son shugabanci a jam'iyyar ta ADC dasu natsu su zama cewa sun samu alkibla da hafin kai. Akwai Atiku Abubakar, Peter Obi, Rotimi Amaechi da duka suka bayyana son tsayawa takarar shugaban kasa a jam'iyyar ta ADC.
Gwamnatin Amurka zata fara bukatar ‘yan Najeriya dake son zuwa kasar su ajiye dala $15,000(Naira Miliyan Asihirin da biyu) idan mutum ya dawo gida za’a mayar masa da kudinsa, idan kuma ya ki dawowa za’a rike kudin

Gwamnatin Amurka zata fara bukatar ‘yan Najeriya dake son zuwa kasar su ajiye dala $15,000(Naira Miliyan Asihirin da biyu) idan mutum ya dawo gida za’a mayar masa da kudinsa, idan kuma ya ki dawowa za’a rike kudin

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka na shirin kakabawa kasashen Duniya sabuwar doka ta shiga kasarta. Kasashen da wannan sabuwar dokar zata shafa sune kasashen da basu da cikakkun bayanai na 'yan kasarsu da kuma wadanda 'yan kasarsu ke yawan zuwa Amurka basa komawa kasashen su na haihuwa. Yawanci wadanda abin zai shafa sune masu zuwa Amurka dan yawon shakatawa ko kasuwanci. Dokar tace za'a bukaci mutane su rika ajiye dala $15,000, kwatankwacin Naira Miliyan 22 kenan, idan sun je Amurka sun ki dawowa gida Najeriya ko kasashensu na Asali, za'a rike kudin, amma idan sun dawo gida, za'a mayar musu da kudadensu. Badai a bayyana sunayen kasashen da lamarin zai shafa ba amma masu sharhi akan al'amuran yau da kullun sun yi ittifakin akwai 'yan Najeriya a ciki.
Shugaba Tinubu ya kashe Naira Biliyan N26.38bn wajan kula da jiragen samansa a cikin watanni 18

Shugaba Tinubu ya kashe Naira Biliyan N26.38bn wajan kula da jiragen samansa a cikin watanni 18

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya karkashin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta kashe akalla Naira Biliyan N26.38bn wajan kula da jiragen saman shugaban kasar a cikin watanni 18 da suka gabata. Hakan na kunshene a cikin rahoton da kungiyar, Govspend ta fitar wadda ke saka ido akan yanda gwamnati ke kashe kudaden Talakawa. Rahoton yace an kashe wadannan kudadenne a tsakanin July 2023 zuwa December 2024. Hakanan rahoton yace shima tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya kashe Naira Biliyan N81.80bn wajan kula da jiragen saman sa a tsakanin shakerar 2016 zuwa 2022.
Kaine Zabin Kanawa a 2027, Jam’iyyar APC reshen jihar Kano ta baiwa shugaba Tinubu tabbaci

Kaine Zabin Kanawa a 2027, Jam’iyyar APC reshen jihar Kano ta baiwa shugaba Tinubu tabbaci

Duk Labarai
Jam'iyyar APC Reshen jihar Kano ta baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tabbacin goyon baya a zaben shekarar 2027 me zuwa. Jam'iyyar ta kuma bayyana Dr. Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam'iyyar a jihar. Sun bayyana hakane yayin wani zama da aka yi a gidan tsohon shugaban jam'iyyar na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Shugaban jam'iyyar a jihar, Alhaji Abdullahi Abbas ya bayyana cewa, an shirya taronne dan warware matsalolin cikin gida na jam'iyyar da kuma shiryawa babban zaben shekarar 2027 dake tafe.
Kalli Bidiyon: Ba yaran nan kadai, har iyayensu ya kamata Shugaba Tinubu ya karramasu>>Inji Sheikh Gadon Kaya

Kalli Bidiyon: Ba yaran nan kadai, har iyayensu ya kamata Shugaba Tinubu ya karramasu>>Inji Sheikh Gadon Kaya

Duk Labarai
Babban Malamin Addinin Islama, Sheikh Abdallah Gadon kaya yayi kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya karrama yara mata da suka yi nasarar lashe gasar Turanci ta Duniya tare da iyayensu. Yace ya kamata a karrama hadda iyayensu saboda yanda suka kula dasu suka basu tarbiyya da ilimi da har suka kai wannan mataki. Malam yace ba 'yan kwallo kadai shugaban kasar zai rika karramawa ba. inda yace shugaban zai bar mummunan tarihi idan bai karrama wadannan yara ba. https://www.tiktok.com/@abdul_prince_/video/7535249986481622328?_t=ZS-8ye0ppEjQ37&_r=1 Wannan kira na malam na zuwane bayan na Sheikh Isa Ali Pantami na cewa ya kamata shugaba Tinubu yawa yaran irin karramawar da yawa 'yan Kwallon Najeriya.