Zulum ya bai wa iyalan sojojin da aka kàshè tallafin miliyan 100
Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai wa iyalan sojijin da aka kashe da kuma waɗanda aka jikkata a fagen daga a yaƙi da ƴan ta da ƙayar-baya a arewa maso gabas, tallafin naira miliyan 100.
Gwamnan ya bayar da tallafin ne ranar Asabar yayin liyafar cin abinci a daidai lokacin da ake ci gaba da bukukuwan sallah, inda babban hafsan sojin ƙasa Laftanar-Janar Olufemi Oluyede da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar suka halarci liyafar a barikin sojoji na Maimalari a Maiduguri.
Zulum ya gabatar da chekin kuɗin na naira miliyan 100 ga hannun kwamandan dakarun Haɗin-Kai, Manjo-janar Abdussalam Abubakar.
Ya bayyana cewa kowane soja da aka raunata a fagen daga zai samu naira 500,000, yayin da za a raba sauran kuɗin ga iyalan sojojin da aka kashe.
Gwamna Zulu...








