Saturday, December 20
Shadow
In ka cika Kwallon Shege ka fito mu yi dambe a bainar jama’a a ga wanene gwani ni da kai>>Oshiomhole ya gayawa Reuben Abati

In ka cika Kwallon Shege ka fito mu yi dambe a bainar jama’a a ga wanene gwani ni da kai>>Oshiomhole ya gayawa Reuben Abati

Duk Labarai
Tsohon shugaban APC, kuma tsohon gwamnan jihar Edo wanda kuma tsohon shugaban kungiyar Kwadago ta NLC ne, watau Adams Oshiomhole ya nemi tsohon kakakin shugaban kasa, Reuben Abati da ya fito su daku idan ya isa. Ya bayyana hakanne a ganawarsa da gidan Talabijin na Channels TV. Yace hakane bayan da Abati a wata hira da aka yi dashi a Arise TV ya ce shin ko Ifeanyi Okowa ya tambayi Oshiomhole an yafe masa zunubansa kamin komawa APC? A baya dai lokacin yana shugaban APC, Adams Oshiomhole ya taba cewa, duk laifin mutum idan ya shiga APC an yafe masa. Saidai yanzu yace wannan magana da Abati yayi bata dace ba, shi a matsayinsa na Sanata menene hadinsa da binciken me laifi? Sannan yace shin ko Abati yana jin haushin kamun da EFCC suka masa ne bayan saukar Jonathan daga Mulki, yac...
An sake Kai wani mummunan hari jihar Filato

An sake Kai wani mummunan hari jihar Filato

Duk Labarai
An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da fiye da shanu 100 a jerin hare-haren da aka kai kan makiyaya a ƙauyuka biyu da ke cikin Kananan Hukumomin Jos na Kudu da Jos na Arewa na Jihar Filato. Hare-haren, wanda ake zargin wasu ’yan bindiga ne suka kai ta hanyar buɗe wuta kan makiyayan da ke kiwo, sun sake jaddada yadda tsaro ya taɓarɓare a yankunan da ke fama da rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, rikice-rikicen da a kullum ke janyo asarar rayuka da dukiyoyi. Sakataren ƙungiyar Miyetti Allah (MACBAN) reshen jihar, Ibrahim Yusuf Babayo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya zargi matasa ‘yan kabilar Berom daga ƙauyukan da abin ya shafa da hannu a hare-haren. Sai dai shugabancin ƙungiyar matasan Berom ya musanta zargin, inda suka bayyana shi a matsayin farfagand...
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya bayar da Umarnin a dauki matasa 130,000 aiki dan su shiga daji su gama da ‘yan Bìndìgà da ake fama dasu

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya bayar da Umarnin a dauki matasa 130,000 aiki dan su shiga daji su gama da ‘yan Bìndìgà da ake fama dasu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabuwar rundunar masu tsaron dazuka a ƙasar baki ɗaya, domin tinkarar matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a Najeriya. A karkashin wannan shiri, za a ɗauki sama da masu tsaro 130,000 da za su kasance da kayan yaƙi da horo na musamman domin kare dazukan ƙasar guda 1,129. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da ta fito daga mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Sunday Dare, wanda ya wallafa ta a shafinsa na X. Sanarwar ta ce "Wannan mataki na tsaro an amince da shi ne yayin taron majalisar zartarwa ta tarayya da aka gudanar ranar Litinin.' "A cikin wannan tsari, shugaba Tinubu ya umurci kowace jiha da ta ɗauki ma’aikata tsakanin 2,000 zuwa 5,000 domin zama masu tsaron daji, dangane da ƙa...
Dalilin da ya sa na koma fashi bayan na yi zaman gidan yari – Matashi

Dalilin da ya sa na koma fashi bayan na yi zaman gidan yari – Matashi

Duk Labarai
Wani matashi mai shekaru 28 da haihuwa, Olayinka Olwaseyi, da aka kama da laifin yi wa masu ababen hawa fashi a danja, ya amsa cewa ya koma aikata laifuka ne saboda rashin aikin yi. Wanda ake zargin, wanda aka sake kama shi watanni uku bayan fitowar sa daga gidan yari, ya yi ikirarin cewa ya so ya daina aikata laifuka amma yunwa ta tilasta masa komawa ruwa. “Ba zan koma fashi ba idan da ina da abin yi, komai kankantarsa. “Bani da aikin yi lokacin da na fito daga gidan yari, mutane sun fara guje min, babu wanda yake so ya yi mu'amala da ni. Mutane ne su ka tilasta min na koma ruwa,” inji shi. An kama Olayinka ne a ranar 13 ga Mayu, 2025, a lokacin da ya ke yunkurin yi wa wani direban mota fashi a kan gadar Mile 12, Legas. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar ...
Ji dabarun da Shugaba Tinubu ke amfani dasu wajan jawo hankalin ‘yan Adawa zuwa APC

Ji dabarun da Shugaba Tinubu ke amfani dasu wajan jawo hankalin ‘yan Adawa zuwa APC

Duk Labarai
Kusan za a iya cewa da wuya gari ya waye a Najeriya ba tare da ƴan siyasa daga jam'iyyun hamayya sun sauya sheƙa zuwa jam'iyya mai mulki ba, walau dai a matakin tarayya ko kuma jihohi da ƙananan hukumomi. Sauya sheƙa zuwa jam'iyya mai mulki ta APC da ya fi bai wa ƴan Najeriya mamaki a baya-bayan nan shi ne na ]tsohon ɗantakarar mataimakin shugaban ƙasa na babbar jam'iyya mai hamayya ta PDP, kuma tsohon gwamnan jihar Delta, Sanata Efeanyi Okowa tare da gwamnan jihar mai ci, Sheriff Oborevwori. Bugu da ƙari, ko a wannan makon ma sai da jam'iyyar mai mulki ta karɓi sabbin masu sauya sheƙa daga jam'iyyar hamayya ta PDP daga jihar Kebbi, inda duka ƴan majalisar dattawan jihar suka koma APC. Wannan ya janyo ƴan Najeriya ke neman sanin irin dubarun da jam'iyya mai mulkin ke bi wajen...
Kaɗan Kenan Daga Cikin Kyaututtukan Raguna Da Shanu Da Masoya Suka Yiwa Ango Rarara Da Amaryasa A’isha Humaira.

Kaɗan Kenan Daga Cikin Kyaututtukan Raguna Da Shanu Da Masoya Suka Yiwa Ango Rarara Da Amaryasa A’isha Humaira.

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kaɗan Kenan Daga Cikin Kyaututtukan Raguna Da Shanu Da Masoya Suka Yiwa Ango Rarara Da Amaryasa A'isha Humaira.
Da Gwamnan Bauchi ya mike tsaye yace zai mare ni, na duba naga ko warewa muka yi bai iya dukana shiyasa nima na mike tsaye na nuna mai tsawona>>Inji Ministan Harkokin kasashen Waje Yusuf Tuggar

Da Gwamnan Bauchi ya mike tsaye yace zai mare ni, na duba naga ko warewa muka yi bai iya dukana shiyasa nima na mike tsaye na nuna mai tsawona>>Inji Ministan Harkokin kasashen Waje Yusuf Tuggar

Duk Labarai
A karon farko cikin makonni da dama, Ministan Harkokin Wajen Najeriya Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya bayyana wa BBC dalilin rigimar da suka yi tsakaninsa da Gwamnan jiharsa ta Bauchi da kuma mataimakin Gwamnan. Tun a baya wasu rahotanni sun ce an samu hatsaniya ne tsakanin Ministan da Gwamna Bala Mohammed, Kauran Bauchi inda har mataimakin gwamnan ya yi yunkurin marin Ministan. Lamarin dai ya faru ne ranar Juma'a 19 ga watan Afirilun nan, lokacin da Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ke wata ziyara a jihar ta Bauchi. A tattaunawarsa da BBC, Ministan ya yi karin haske kan abin da ya haddasa rashin jituwa tsakaninsu har ta kai su ga sa-in-sa. Ministan ya ce ba kamar yadda wasu ke yadawa ba cewa da mataimakin gwamna suka yi hatsaniya, da ainahin shi gwamnan ne abin y...
Kalli Bidiyon yanda shugaban jarabawar JAMB ya fashe da kuka saboda kuskuren hukumar yasa dalibai da yawa sun fadi jarabawar

Kalli Bidiyon yanda shugaban jarabawar JAMB ya fashe da kuka saboda kuskuren hukumar yasa dalibai da yawa sun fadi jarabawar

Duk Labarai
An gano cewa, Kuskuren hukumar shirya jarabawar share fagen shiga jami'a ta JAMB yasa dalibai da yawa sun fadi jarabawar. Akalla Dalibai Miliyan 1.5 ne suka ci kasa da makin da ake bukata a jarabawar ta bana wadda ake ganin sun yi yawa. A yayin taron manema labarai dan bayyana dalilin da yasa aka samu wannan tangarda, shugaban hukumar ta JAMB, Professor Ishaq Oloyede ya fashe da kuka. https://twitter.com/ARISEtv/status/1922676757787766804?t=LRtY04XWaym5mjx3aoC7Ug&s=19 Ya dai bayar da hakuri sannan kuma ya sha Alwashin sakewa dalibai da yawa jarabawar. Yankin da aka samu wannan matsaloli na jihar Legas ne da kudu maso kudu.
Kalli Bidiyo: Dangote na daya daga cikin wadanda suka gaisa da shugaban Amurka, Donald Trump a kasar Qatar

Kalli Bidiyo: Dangote na daya daga cikin wadanda suka gaisa da shugaban Amurka, Donald Trump a kasar Qatar

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote na daya daga cikin wadanda suka gaisa da Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yin ziyarar da ya kai kasar Qatar. Shugaba Trump ya kao ziyara kasar Qatar bayan kammala ziyara a kasar Amurka. https://twitter.com/thecableng/status/1922724222867996726?t=ELlWm2kvK9sQIMxkMnfH5g&s=19 Kasar Qatar dai ta baiwa shugaba Trump kyautar jirgin sama Kirar Boeing.