Saturday, December 13
Shadow
Zargin Biliyan biyu ga Kwankwaso: Babu hankali da lissafi a maganar Baffa Bichi – Abba Gida-Gida

Zargin Biliyan biyu ga Kwankwaso: Babu hankali da lissafi a maganar Baffa Bichi – Abba Gida-Gida

Duk Labarai
Zargin Biliyan biyu ga Kwankwaso: Babu hankali da lissafi a maganar Baffa Bichi - Abba Gida-Gida. Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi wa tsohon Sakataren Gwamnatin Kano, Baffa Bichi martani bisa zarge-zargen da ya fada akan gwamnatin. A wata hira da manema labarai da ta karade kafafen watsa labarai, an jiyo Baffa Bichi, wanda aka cire shi daga muƙamin sakataren gwamnatin, na cewa an ɗauki matakin ne don ya ki amincewa da ya sahale a rika diban Naira biliyan 2 duk wata ana saka wa a asusun Rabi'u Musa Kwankwaso, jagoran Kwankwasiyya. A wani taro da kansilolin mazaɓu 484 na jihar a yau Lahadi, gwamna Abba ya ce maganganun da Bichi ya yi "babu hankali da lissafi da aiki da ƙwaƙwalwa a wannan maganar." A cewar gwamna Abba, babu hankali a ce gwamnatin sa da ko shekaru bi...
Ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu – Abba Gida-Gida

Ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu – Abba Gida-Gida

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatin sa ba wajen zaman ɓarayi ba ce sabo da jajircewa wajen yaƙi da cin hanci da rashawa. Da ya ke jawabi a wajen taro da kansilolin mazaɓu 484 da ke gudana yanzu haka a gidan gwamnati, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatin sa ba za ta lamunci satar kudin al'umma ba. A cewar sa, ya na jagorantar gwamnati mai tsafta da kaffa-kaffa wajen sace kudin al'umma, inda ya jaddada cewa "ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu," Ya ce wannan kokarin yaki da din hanci ne ya sanya gwamnatin ke samun makudan kuɗaɗen da ta ke ta bijiro da aiyuka domin jin dadin al'ummar Kano. Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Gwamna Yusuf ya fadi hakan ne bayan da a kwanan nan tsohon sakataren gwamnatin, Dakta Abdullahi Baffa Bichi ya ke zargin badakala da wawure kuɗaɗen al'...
A karshe dai, Sanata Natasha Akpoti ta amince da zargin da aka mata na cewa ta baiwa wata kudi dan ta kalawa Sanata Godswill Akpabio Sharri

A karshe dai, Sanata Natasha Akpoti ta amince da zargin da aka mata na cewa ta baiwa wata kudi dan ta kalawa Sanata Godswill Akpabio Sharri

Duk Labarai
Bayan da 'yar jarida Dr. Sandra Duru ta yiwa Sanata Natasha Akpoti Tonon Silili, inda tace sun yi waya kuma ta nadi maganar da suka yi inda Sanata Natasha Akpoti ta mata tayin Miliyan Naira 200 dan ta kalawa Sanata Godswill Akpabio sharrin cewa yana safarar sassan jikin mutane, Sanata Natasha Akpoti ta karyatata. Natasha tace bata ma san 'yar Jaridar ba. Saidai daga baya da aka dameta da tambaya, ta amsa cewa lambar wayar da 'yar Jaridar ta nuna sun yi magana da ita, tatace. Watau kalaman da ake zarginta da furtawa ta furtasu. Ko da dai Sanata Natasha Akpoti ta nace akan cewa bata furta wadancan kalamai ba, to lallai bai kamata mutane su ci gaba da yadda da maganganunta ba.
Barazanar rufe Facebook ta ficewa daga Najeriya ba zai hana mu hukunta su ba – Inji Gwamnati

Barazanar rufe Facebook ta ficewa daga Najeriya ba zai hana mu hukunta su ba – Inji Gwamnati

Duk Labarai
Hukumar da ke sanya ido kan farashi da kare haƙƙin masu sayen kaya ta Najeriya (FCCPC), ta ce barazanar da kamfanin Meta ya yi na ficewa daga ƙasar, ba zai hana a hukunta shi ba. Hukumar ta ce ba za a janye shari'ar da ake yi da Meta ba duk da barazanar da ya yi. FCCPC ta ce kamfanin ya yi barazanar ficewa daga Najeriya ne domin a ji tausayinsa, da kuma matsawa hukumar canza matakin da ya ɗauka na cin tarar kamfanin. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da darektan hukumar, Ondaje Ijagwu ya fitar ranar Asabar. Hakan kuma na zuwa ne bayan wani gargaɗi da Meta ya yi da farko cewa "za a tilasta masa rufe shafukan Facebook da Instagram a Najeriya don kauce wa barazanar fuskantar hukunci". Hukumar ta zargi Meta da yi wa bayanan ƴan ƙasar kutse, ciki har da aika bayanan ba tare d...
Mu Makafine, Kwankwaso ne jagoranmu, Duk inda ya koma zamu bishi>>Inji Shugaban NNPP na Kano, Hashim Dungurawa

Mu Makafine, Kwankwaso ne jagoranmu, Duk inda ya koma zamu bishi>>Inji Shugaban NNPP na Kano, Hashim Dungurawa

Duk Labarai
Shugaban jam'iyyar NNPP reshen jihar Kano, Hashim Dungurawa ya bayyana cewa, duk inda Kwankwaso ya tafi suna tare dashi. Ya bayyana hakanne a yayin ganawa da manema labarai na jaridar Leadership a yayin da ake tambayarsa game da yiyuwar komawar Kwankwaso wata jam'iyya. Yace su dukansu makafi ne Kwankwaso ne jagoransu dan haka duk inda ya tafi zasu bishi. Yace duk abinda Kwankwaso ya musu daidai ne dan haka su basu da zabi sai nashi, idan ya canja jam'iyya zasu bushi.
Ni da nasan Allah zai Tambayeni dan haka bana tsoron wata EFCC a shirye nake in amsa tambayoyinsu>>Tsohon Shugaban NNPCL,Mele Kolo Kyari

Ni da nasan Allah zai Tambayeni dan haka bana tsoron wata EFCC a shirye nake in amsa tambayoyinsu>>Tsohon Shugaban NNPCL,Mele Kolo Kyari

Duk Labarai
Tsohon shugaban kamfanin mai na kasa, NNPCL, Mele Kolo Kyari ya bayyana cewa ya gudanar da aikinsa da tsoron Allah a zuciya. Yace a shirye yake ya amsa tambayoyin EFCC dan yasan Akwai tambayoyin Allah ma da zai amsa. Ya bayyana hakane a martanin da yayi ta X kan cewa, EFCC sun kamashi. Mele Kyari yayi kira ga kafafen yada labarai da su guji yada labarin da bai inganta ba.
Yanzu na yadda tabbas akwai matsalar tsaro a kasarnan>>Shugaba Tinubu

Yanzu na yadda tabbas akwai matsalar tsaro a kasarnan>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, ya yadda akwai matsalar tsaro a Najeriya. Ya bayyana hakane a ziyarar da ya kai jihar Katsina. Shugaban ya sha Alwashin yin amfani da dukkan kayan yaki na zamani da sauransu dan magance matsalar tsaron da ake fama da ita. Ya jadda cewa, idan ba'a magance matsalar tsaro ba, masu zuba jari ba zasu iya zuwa Najeriya ba.
Kalli Bidiyo da Hotuna: Yanda ‘yan tà’adda suka kai hari sansanin sojoji a jihar Yobe, sun kàshè sojoji 4 da kona motocin yakin sojojin, daga farkon shekara zuwa Yanzu, Rahotanni sun bayyana cewa sun tashi sansanin sojoji sama da 8

Kalli Bidiyo da Hotuna: Yanda ‘yan tà’adda suka kai hari sansanin sojoji a jihar Yobe, sun kàshè sojoji 4 da kona motocin yakin sojojin, daga farkon shekara zuwa Yanzu, Rahotanni sun bayyana cewa sun tashi sansanin sojoji sama da 8

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana a baya cewa, mayakan kungiyar Ìśìśì sun dauki alhakin kai harin da yayi sanadiyyar mutuwar sojojin Najeriya 4 da jikkata wasu a jihar Yobe. Kungiyar ta kuma wallafa hotunan harin da ta yi ikirarin kaiwa. An ga hotunan konannun motocin sojoji yayin da wasu kuma aka ga suna ci da wuta. https://twitter.com/Sazedek/status/1918787069247132094?t=xhNqOFWtBQr7VEQh5qsw1Q&s=19 Kungiyar ta yi ikirarin kai hari da tarwatsa sansanin sojoji sama da 10. Saidai Maau shashi sun ce sansanin sojoji 8 ne suka tarwatsa daga farkon shekararnan zuwa yanzu.