Tuesday, December 16
Shadow
Kalli Bidiyo: An zargi Ana yiwa kananan yara maza fyade a gidan yarin Goron Dutse dake Kano

Kalli Bidiyo: An zargi Ana yiwa kananan yara maza fyade a gidan yarin Goron Dutse dake Kano

Duk Labarai
Wani faifan Bidiyo ya bayyana inda aka ji wani bawan Allah na ikirarin cewa ana yiwa yara maza fyade a gidan yarin Goron Dutse dake Kano. Yace ana amfani da kananan shekaru da yaran ke da su da kuma bukata ta abinci da suke da ita ana lalata dasu. Yace a wasu lokutan ma ana hada baki da wasu bata garin ma'aikatan gidan yarin ana basu kudi ana baiwa yaran a daukesu, yace a wasu lokutan kuma yawan kudin da za'a baiwa yaranne ke daukar hankalinsu su aikata wannan masha'a. https://twitter.com/bapphah/status/1918931313190412518?t=Ul1rceH1xKpQnZ_oIIHdpQ&s=19 Yace yana kira ga hukumomi da su je su bincika abubuwan da ya fada inda yace akwai ma abubuwan da bai fada ba wanda ake yi a gidan yarin.
Ba gaskiya bane cewa bama ciyar da masu laifi abinci me kyau, Abinci me rai da lafiya muke basu>>Hukumar Gidajen Gyara Hali ta Najeriya

Ba gaskiya bane cewa bama ciyar da masu laifi abinci me kyau, Abinci me rai da lafiya muke basu>>Hukumar Gidajen Gyara Hali ta Najeriya

Duk Labarai
Hukumar Gidajen Gyara Hali ta Najeriya ta musanta ikirarin dake cewa, tana ciyar da masu laifi abinci da bashi da sinadaran gina jiki. Kakakin hukumar, Abubakar Umar, ne ya bayyana hakan. Yace Rahoton ba gaskiya bane, suna bin doka da oda wajan ciyar da masu laifi abinci kamar yanda aka tanadar. Yace kuma kwanannan gwamnati ta kara yawan kudin ciyar da kowane me laifi zuwa Naira ₦1,125 a kullun. Yace ba a boye suke baiwa masu laifi abinci ba, akwai kungiyoyin kare hakkin al'umma da hukumomi na cikin gida da kasashen waje dake saka ido kan yanda ake ciyar da masu laifin amma basu bayar da wani korafi kan yanda ake ciyar da masu laifin ba
Babu Abinda matasan Najeriya suka iya sai Korafi da zagin Shuwagabanni>>Inji Sanata Ireti Kingibe

Babu Abinda matasan Najeriya suka iya sai Korafi da zagin Shuwagabanni>>Inji Sanata Ireti Kingibe

Duk Labarai
Sanata Ireti Kingibe ta koka da cewa, Babu abinda matasan Najeriya suka iya sai korafi da zagin shuwagabannin. Tace idan aka yi abu wani lokacin sai matasan su ce zasu yi zanga-zanga amma basa iyawa. Tace wannan kasa taku ce, baku da wata kamarta, dan haka ya kamata ku tashi tsaye ku gyarata. Tace amma yawanci ko Talakawa sun je kusa da masu mulki, yawanci suna neman abinda zai amfanesu ba ba wanda zai amfani Al'umma ba.

Ƴan Sa Kai 11 Sun Ràsà Rayukansu a Sokoto Bayan Artabu da Ƴan Bìndìgà

Duk Labarai
Ƴan Sa Kai 11 Sun Rasa Rayukansu a Sokoto Bayan Artabu da Ƴan Bindiga ‎‎Aƙalla ‘yan sa-kai 11 ne aka tabbatar sun mutu, wasu da dama kuma ba'a san inda suke ba, bayan wani mummunan artabu da suka yi da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a karamar hukumar Tangaza da ke Jihar Sokoto.‎‎Rikicin ya fara ne tun ranar Juma’a, inda aka samu rahoton mutuwar mutane biyu, amma daga bisani aka ƙara gano gawawwaki tara a dajin Lakurawa. Har yanzu ana ci gaba da neman wasu da ba a san inda suke ba, tare da taimakon sojoji da jami’an tsaro daga Binji da Racca.‎‎Shaidun gani da ido sun bayyana cewa rikicin ya fara ne bayan da ‘yan sa-kai suka hana wani hari a kauyen Magonho, lamarin da ya janyo musayar wuta mai tsanani.‎‎Ƴan bindigar, wadanda yawansu ya kai 40, sun zo ne akan babura guda 20 dauke da ma...
Yunwa da talauci, fatara, rashin tsaro sun addabi mutanen arewa Amma ana yunwa Tinubu Waka Yana anashuwa, Yana holewa. Babu Kimi. Akwai ranar kin dillanci>>Inji Mahadi Shehu

Yunwa da talauci, fatara, rashin tsaro sun addabi mutanen arewa Amma ana yunwa Tinubu Waka Yana anashuwa, Yana holewa. Babu Kimi. Akwai ranar kin dillanci>>Inji Mahadi Shehu

Duk Labarai
Yunwa da talauci, fatara, rashin tsaro sun addabi mutanen arewa Amma ana yunwa Tinubu Waka Yana anashuwa, Yana holewa. Babu Kimi. Akwai ranar kin dillanci. https://twitter.com/shehu_mahdi/status/1918965226831028383?t=QHuXUJuRhgcAO6N_1YVNTg&s=19 Da yawa dai sun bayyana takaici da mamaki irin na Mahadi Shehu.
Shekarar mu daya cur bamu ci nama ko kifi ba, babu abinci me gida jiki babu kulawar Lafiya>>Inji Masu Laifi dake daure a gidan gyara hali

Shekarar mu daya cur bamu ci nama ko kifi ba, babu abinci me gida jiki babu kulawar Lafiya>>Inji Masu Laifi dake daure a gidan gyara hali

Duk Labarai
Masu Laifi dake daure a gidan gyara hali na garin Jos a jihar Filato sun koka da cewa, yanayin da suke ciki ya munana. A wani rahoto da kafar Sahara reporters ta wallafa, mai laifin sunce shekara daya kenan rabonsu da cin nama ko kifi, sai wake wanda babu wani abun gina jiki a cikinsa. Hakanan sun koka da cewa, idan basu da lafiya babu kulawa kuma ana azabtar dashi ga nuna kabilanci. A wani hoto da aka wallafa, an ga kalar abincin da ake baiwa masu laifin wanda ya hada da wake da garin rogo da miyar Kuka.
Gwamnatin Tarayya ta sha Alwashin kammala aikin gina titin jirgin kasa daga Kano zuwa Maradi nan da shekarar 2026

Gwamnatin Tarayya ta sha Alwashin kammala aikin gina titin jirgin kasa daga Kano zuwa Maradi nan da shekarar 2026

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana aniyar gwamnatinsa na kammala gina titin jirgin kasa daga Kano, zuwa Jigawa zuwa Katsina zuwa Maradi. Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne ya bayyana haka a yayin da ya kaddamar da wasu ayyuka a jihar ta Katsina da gwamnatin Jihar ta aiwatar. Shugaban kasar yace idan aka kammala wannan aiki zai taimaka wajan saukaka tafiyar mutane da safarar kaya wanda yace hakan zai rage amfani da Titi. Hakanan shugaban kasar yace sun bayar da aikin gyaran titunan da suka hada Marabar Kankara -Dutsinma -Katsina da kuma wadanda suka hada garuruwan Zaria -Hunkuyi -Dabai da kuma wadanda suka hada garuruwan. Hakanan shugaban kasar yace suna aiki akan titin Kano zuwa Katsina.
Kalli Bidiyo yayin da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ke tambayar Anya Baffa Bichi na da hankali kuwa kan maganar da yayi ta cewa ana baiwa Kwankwaso Biliyan biyu

Kalli Bidiyo yayin da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ke tambayar Anya Baffa Bichi na da hankali kuwa kan maganar da yayi ta cewa ana baiwa Kwankwaso Biliyan biyu

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa Anya Baffa Bichi na da hankali kuwa? Yayi wannan tambayar ne game da ikirarin Baffa na cewa ana turawa Kwankwaso Naira Biliyan 2 duk wata. https://twitter.com/HonAbdullahiM12/status/1919049059119014034?t=cOh5tIQ0hOwP_0-gIyNDoQ&s=19 Wannan magana dai ta jawo cece-kuce sosai a kafafen sadarwa