Saturday, April 11
Shadow
Kalli yanda Dangote ya raka gawar Kawunsa Aminu Dantata zuwa Madina

Kalli yanda Dangote ya raka gawar Kawunsa Aminu Dantata zuwa Madina

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya raka gawar kawunsa, Aminu Dantata daga Abu Dhabi kasar UAE zuwa Birnin Madina na kasar Saudiyya. Aminu Dantata ne daya daga cikin kawun Dangote Dangote na karshe da suka rage masa. https://twitter.com/SasDantata/status/1939963458931376381?t=OVEul28Z6bHYsZCZFuO5rw&s=19 Bayan sallar la'asar a kasar Saudiyya da misalin karfe 1:30 a Najeriya ne za'a yi jana'izar Marigayin.
Da Duminsa: An bayyana lokacin da za’awa gawar Marigayi Aminu Dantata sallah a Madina

Da Duminsa: An bayyana lokacin da za’awa gawar Marigayi Aminu Dantata sallah a Madina

Duk Labarai
Bayan sallar La'asar a ranar Talata ne ake sa ran za a gudanar da jana'izar fitaccen attajirin nan Alhaji Aminu Ɗantata a masallacin Madina. Mustapha Junaid, mataimaki na musamman ga marigayin ya shaida wa BBC cewa shirye-shirye sun kammala domin gudanar da jana'izar. "Alhamdu lillah an ɗauki marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga filin jirgi na Madina kuma yanzu haka za a je Shakzura inda a nan ne za a ƙarasa shirya shi kafin daga bisani a kai shi haramin Madina domin gudanar da sallah kamar yadda hukumomin Saudiyya suka amince." In ji Mustapha Junaid. A ranar Asabar ne shahararren ɗankasuwa Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekara 94 da haihuwa a shekarar miladiyya. A shekarar Hijira (ta Musulunci) kuma, ya rasu yana da shekara 97, kamar yadda sakatarensa Mustapha Abdullahi ya shaid...
Da gaske Sarki Sanusi II ne zai yiwa Mariya Aminu Dantata sallar Gawa? Ji bayani dalla-dalla

Da gaske Sarki Sanusi II ne zai yiwa Mariya Aminu Dantata sallar Gawa? Ji bayani dalla-dalla

Duk Labarai
Rahotanni nata yawo a kafafen sada zumunta inda ake yada cewa, sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ne zai yiwa gawar Marigayi Aminu Dantata Sallah a birnin Madina. Hakan na zuwane yayin da rahotanni ke cewa, Sarki Aminu Ado Bayero ma yace Santata ya bar masa wasiyyar cewa shine zai masa sallah. A yanzu dai gawar marigayi Aminu Dantata ta isa Birnin Madina kuma ana jiran mahukunta birnin ne su bayyana lokacin da za'a masa sallah. A hukumance, ba'a sanar da wanene zaiwa gawar Marigayi Aminu Dantata Sallah ba.
Kalli Bidiyo Da Duminsa: Gawar Marigayi Dantata ta Isa Madina da safiyar yau

Kalli Bidiyo Da Duminsa: Gawar Marigayi Dantata ta Isa Madina da safiyar yau

Duk Labarai
Rahotanni daga Madina birnin Ma'aiki na cewa, gawar marigayi Aminu Dantata ta isa birnin. Bayan Saukar Gawar Marigayi Alh Aminu Dantata Tareda da Iyalensa; Alh Tajudeen Dantata da Hassan Dantata da Yaya, Jikoki da Yan Uwa Da Abokan Arziki duk Suna Wannan Guri Domin Mika Marigayi zuwa ga Ma'aikatan Kula Da Makabartar Baki'ah Inda akesa Rai Zasuyi masa Suttura. Allah yajikan sa Da Rahma. https://twitter.com/GASHASHCOLLECT2/status/1939964376754057576?t=i0_KkOxpnECK4Dy5VN-ZiQ&s=19 Me magana da yawunsa yace zasu jira hukumomin Madina au basu lokacin da za'a masa sallah.
Kalli Bidiyo Da Duminsa: An Sàcè kanin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare>>Inji Mahdi Shehu

Kalli Bidiyo Da Duminsa: An Sàcè kanin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare>>Inji Mahdi Shehu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Dan siyasa, Mahdi Shehu yace an sace kanin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare. Ya bayyana hakane a shafinsa na X inda ya wallafa Bidiyon wani mutum da aka gani zagaye da 'yan Bindiga rike da muggan makamai yana fadar cewa uwarsu daya ubansu daya da Gwamnan jihar Zamfara. Mahdi dai yayi tambayar cewa shin ko Gwamnan zai biya kudin fansa. Ko kuwa zai yi sulhu da 'yan Bindigar? Kalli Bidiyon anan Babu dai wata sanarwa data tabbatar da cewa wannan mutumin dan uwa...
Matatar man Dangote ta kara rage farashin man fetur dinta

Matatar man Dangote ta kara rage farashin man fetur dinta

Duk Labarai
Matatar man fetur din Dangote ta rage farashin man fetur dnta inda a yanzu take sayar dashi akan Naira 840 maimakon 880 da yake a baya. Hakan na wakiltar ragin kaso 4.5. Bincike ya bayyana cewa Dangote ya rage farashin nasa ne bayan da farashin danyen man fetur ya fadi a kasuwar Duniya zuwa dala $67.50 daga Dala sama da $70 da yake a baya. Wasu sauran kamfanonin ma sun rage farashin man fetur din nasu kamar yanda Dangote yayi.
Shin wai ina Kwankwaso? Ana ta cece-kuce bayan da manyan mutanen Kano suka je jana’izar Aminu Dantata Madina amma ba’a ga Kwankwaso ba

Shin wai ina Kwankwaso? Ana ta cece-kuce bayan da manyan mutanen Kano suka je jana’izar Aminu Dantata Madina amma ba’a ga Kwankwaso ba

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Yayin da manyan mutanen jihar Kano suka hallara a Madina wajan jana'izar Marigayi Aminu Dantata, ana ta daga wuya dan ko za'a hango Kwankwaso amma ba'a ganshi ba. Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya jagoranci tawagar Gwamnan Jigawa da Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero zuwa jana'izar. Da yawa sun yi tsammanin za'a ga Kwankwaso a cikin tawagar amma ba'a ganshi ba. Hakan yasa ake ta cece-kuce akai. Wasu dai na ganin zuwan Abba Gida-Gida ya isa ya wakilci Kwankwa...
Ji Bayani Dalla-Dalla: Shin waye zaiwa gawar marigayi Dantata Sallah a Madina?

Ji Bayani Dalla-Dalla: Shin waye zaiwa gawar marigayi Dantata Sallah a Madina?

Duk Labarai
A yayin da manyan mutane musaman daga jihar Kano suka hallara a Madina dan halartar jana'izar marigayi Aminu Dogo, Dantata. Ana tababar wanene zai yiwa marigayin sallar gawa? Wasu rahotanni sun ce marigayin ya bar wasiyyar tsohon sarkin Kano, Aminu Ado Bayero ya mai sallar gawa wanda tuni shima yana can Madina. Saidai Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II duk suma suna can Madinan. Zuwa anjima zami samu bayani kan yanda ta kaya.
Kalli Bidiyon: Shima tsohon shugaban APC, Ganduje ya tafi Madina dan halartar jana’izar Dantata

Kalli Bidiyon: Shima tsohon shugaban APC, Ganduje ya tafi Madina dan halartar jana’izar Dantata

Duk Labarai
Rahotanni daga Madina na cewa, Tsohon shugaban jam'iyyar APC da tawagarsa sun isa birnin dan halartar jana'izar Marigayi Aminu Dantata. A cikin tawagar Ganduje akwai sanata Barau Jibrin da sauransu. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan saukar Ganduje daga shugabancin jam'iyyar APC. https://twitter.com/tudunwada__mi/status/1939767084486951292?t=xz6XVz4xauDslIATf5EErw&s=19 Sauran wanda suka tafi Madina sun hada da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, Gwamnan jihawa, Umar Namadi, da sauransu. Akwai kuma tawagar shugaban kasa wadda ministan tsaro, Abubakar Badaru ya jagoranta. Tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero shima ya tafi Madinan.
APC ta saka Naira Miliyan 20 a matsayin kudin fom din takarar Sanata sannan Naira Miliyan 10 a matsayin kufin Fom din takarar dan majalisar wakilai

APC ta saka Naira Miliyan 20 a matsayin kudin fom din takarar Sanata sannan Naira Miliyan 10 a matsayin kufin Fom din takarar dan majalisar wakilai

Duk Labarai
Jam'iyyar APC ta saka Naira Miliyan 20 a matsayin kudin sayen fom din takarar sanata sannan ta sa Naira Miliyan 10 a matsayin kudin fom din takarar dan majalisar wakilai a zabukan cike gurbi da ake shirin yi. Hakan na kunshene a cikin takardar bayanan ya da za'a gudanar da zaben da jam'iyyar ta fitar ta hannun babban sakatarenta, Sulaiman Argungu. Fom din tsayawa takarar dan majalisar jiha kuwa an sakashi akan Naira Miliyan 2. Matasa dake tsakanin shekaru 25 zuwa 40 zasu samu ragin kaso 50 cikin 100 na kudin sayen fom din. Jam'iyyar tace tana sayar da fom din a ofishinta dake Wuse II, Abuja