Sunday, February 15
Shadow
A shekarar 1983 manyan sojoji sun sameni suka ce zasu yiwa Tsohon Shugaban kasa, Shehu Shagari Juyin mulki dan in zama shugaban kasa amma nace bana so>>Inji Obasanjo

A shekarar 1983 manyan sojoji sun sameni suka ce zasu yiwa Tsohon Shugaban kasa, Shehu Shagari Juyin mulki dan in zama shugaban kasa amma nace bana so>>Inji Obasanjo

Duk Labarai
Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa, a shekarar 1983, manyan sojoji sun sameshi suka ce zasu yiwa shugaban kasa a wancan lokacin, Shehu Shagari Juyin Mulki dan shi Obasanjon ya zama shugaban kasa. Saidai Obasanjon yace musu baya so. Yace dalilinsa shine su suka Kafa Dimokradiyya diyya a Najeriya dan haka ba zai zama cikin wanda zasu rusata ba. Hakanan shima tsohon shugaban kasar Soji, Janar Ibrahim Badamasi ya tabbatar da wannan labari na Obasanjo.
Da Duminsa: Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya bayyana Muguntar da DSS suka shirya mai da zarar an bayar da Belinsa

Da Duminsa: Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya bayyana Muguntar da DSS suka shirya mai da zarar an bayar da Belinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar 'yansandan Farin kaya ta DSS na shirin sake kama tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami da zarar an bayar da belinsa. Malami ne ya bayyana hakan ta bakin me magana da yawunsa, Muhammed Bello Doka. Yace DSS na shirin yi masa wannan abu da ya kira take hakinsa ne bayan da kotu ta bayar da belinsa. Malami yayi zargin cewa, DSS sun dana tarko akansa suna jiran a bayar da belinsa su sake chafkeshi.
Da Duminsa:Wata Majiya ta bayyana ainahin Abinda Kwankwaso yaso yiwa Abba wanda shine ya baiwa Abban Haushi yasa yake son komawa APC

Da Duminsa:Wata Majiya ta bayyana ainahin Abinda Kwankwaso yaso yiwa Abba wanda shine ya baiwa Abban Haushi yasa yake son komawa APC

Duk Labarai
Wata majiya daga Kano tace ainahin abinda ya kawo rashin jituwar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da shugaban Tafiyar Kwankwasiyya, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso shine. Kwankwason ya so saka 'yan majalisar jihar Kano su tsige Abba. Wannan banai na ta yawo ne a kafafen sada zumunta inda a wata majiyar kuma aka rika ruwaito cewa, Kwankwaso baya son Abba ya sake tsayawa takarar Gwamnan Kano ne a shekarar 2027 inda yake son kawo wani dan takara na daban. https://twitter.com/i/status/2008888990062223473 https://twitter.com/i/status/2008973814240055306
Tsohon Mataimakin Peter Obi a zaben 2023>>Yusuf Datti Baba Ahmad ya fito takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party

Tsohon Mataimakin Peter Obi a zaben 2023>>Yusuf Datti Baba Ahmad ya fito takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin Peter Obi a zaben shugaban kasa na shekarar 2023, Yusuf Datti Baba Ahmad ya bayyana cewa, zai fito takarar shugaban kasa zaben shekarar 2027 a jam'iyyar Labour Party. Ya bayyana cewa idan ya zama shugaban kasa, a watanni na farko zai tabbatar ya linka Albashin jami'an tsaro da sau 4. https://twitter.com/i/status/2008929943150071954
Kotu ta bayar da Umarnin EFCC ta rike kadarorin Abubakar Malami 57

Kotu ta bayar da Umarnin EFCC ta rike kadarorin Abubakar Malami 57

Duk Labarai
Kotun tarayya dake da zama a Abuja ta amincewa hukumar EFCC ta ci gaba da rike kadarorin tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami. Kotun tace EFCC ta rike kadarorin guda 57 na wucin gadi kamin a amince a kwacesu na dindindin. Hakanan Kotun ta bayar da belin Malami da dansa da matarsa. Hakanan a zaman kotun, Mai Shari'a, Justice Emeka Nwite ya Gargadi Lauyan Abubakar Malami cewa kada ya sake yace zai nemi wata Alfarma a wajansa. Yace ba zai lamunce a bata masa suna ba kuma duk sanayyarsa da mutum idan aka zo wajan aiki zai nuna ba sani ba sabo.
Abin Kunya: ‘Yan Kwallon Najeriya, Super Eagles sun ce ba zasu je buga wasan su da Algeria ba idan ba’a biyasu hakkokinsu ba

Abin Kunya: ‘Yan Kwallon Najeriya, Super Eagles sun ce ba zasu je buga wasan su da Algeria ba idan ba’a biyasu hakkokinsu ba

Duk Labarai
Kungiyar 'yan kwallon Najeriya ta Super Eagles da masu horas dasu sun ce ba zasu je wasan da zasu buga da Algeria ba idan ba'a biyasu hakkokinsu ba. Kungiyar ta bayyana cewa akwai alkawuran kudaden da aka musu idan suka yi nasara a wasanni da kasashen Tanzania, Tunisia, Uganda, da Mozambique amma ba a cika musu wadannan alkawuran ba. Kungiyar tace ba zata ke garin Marrakech ba ranar Alhamis dan yin Atisayen wasan da zasu buga da kungiyar kasar Algeria ba idan ba'a biyasu ba. Najeriya dai zata yi wasan Quarter finals da kasar Algeria.
Kalli Bidiyon: Ni kirista ne amma na zama Musulmi

Kalli Bidiyon: Ni kirista ne amma na zama Musulmi

Duk Labarai
Wannan Kiristan ya bayyana cewa, ya Musulunta, saidai yace shi mawaki ne Yace babban dalilinsa na komawa Musulmi shine dan wakarsa ta samu daukaka. https://www.tiktok.com/@funnyalpha/video/7592315088418229524?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7592315088418229524&source=h5_m&timestamp=1767796279&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7568740291232040721&share_link_id=3704f903-f8e3-4f92-8cbe-059cd3640d9e&share_app_id=1233&ugbiz_name=MAIN&ug_btm=b8727%2Cb2878&link_r...
Wani na Kusa da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari yayi magana kan Malamin da aka ce yana son auren Hajiya A’isha Buhari

Wani na Kusa da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari yayi magana kan Malamin da aka ce yana son auren Hajiya A’isha Buhari

Duk Labarai
Bashir Ahmad yayi magana kan jita-jitar auren Shiekh Pantami da Aisha Buhari Wannan ba labari ba ne da ya kamata ma a tsaya ana ƙoƙarin ƙaryata shi, domin duk wani mai hankali ba zai ɗauke shi da muhimmanci ba. Sai dai tunda har yanzu wasu na ci gaba da yaɗa wannan jita jitar, ya zama dole a fayyace gaskiya. Labarin da wasu ke yadawa cewa Hajiya Aisha Buhari ta amince za ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ce tsagwaronta. Babu ko ƙwayar gaskiya a cikinsa kwata-kwata. -inji Bashir Ahmad tsohon hadimin margayi Buhari Me zaku ce? Daga Kafar Ayau News