Friday, December 5
Shadow
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle yace Sojan Ruwa da ya tare Nyesom Wike bai aikata laifin komai ba

Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle yace Sojan Ruwa da ya tare Nyesom Wike bai aikata laifin komai ba

Duk Labarai
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya bayyana cewa, sojan ruwa, A. Yerima da ya tare Ministan babban birnin tarayya, Abuja Nyesom Wike bai aikata laifin komai ba. Minista Bello Matawalle ya bayyana cewa sojan na bakin aikinshi ne kuma yana bin umarnin me gidansa ne. Bello Matawalle ya bayyana hakane a hirar da aka gudanar dashi a gidan Talabijin na DCL Hausa. Ya kuma kara da cewa, Wike yayi hattara dan kuwa wulakanta sojan da yayi kamar ya wulakanta shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne.
Kalli Bidiyon: Sojan Ruwa A. Yerima be yi wani kokari ba abinda yawa Wike>>Inji Seun Kuti

Kalli Bidiyon: Sojan Ruwa A. Yerima be yi wani kokari ba abinda yawa Wike>>Inji Seun Kuti

Duk Labarai
Dan Gidan Marigayi mawaki, Fela Kuti, Watau Seun Kuti ya bayyana cewa, shi bai ga kokarin matashin Soja, A. Yerima da ake ta yayatawa ba. Yace inda ya kamata sojan yayi kokari shine da aka Turashi tsaron Filin yacewa Ogansa ba abinda kundin tsarin Mulkin kasa yace yayi ba kenan. Saidai da yawa basu yadda da Seun Kuti ba game da wannan ra'ayi nasa. https://twitter.com/General_Somto/status/1988879155677524470?t=XgFmAtUOE4WmLLTeWHoEyg&s=19
Saida muka gargadi Wike kada ya je waja da Soja Yerima yake amma yakiya, Dan haka abinda sojan yayi abin yabawa ne>>Inji Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle

Saida muka gargadi Wike kada ya je waja da Soja Yerima yake amma yakiya, Dan haka abinda sojan yayi abin yabawa ne>>Inji Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle

Duk Labarai
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya bayyana cewa, sai da suka gargadi Wike kada ya je ya fuskanci sojan ruwa, A. Yerima ya bari sojoji su kammala bincikensu akan filin amma yaki ya. Yace abinda sojan yayi ya aikata daidai bai aikata laifi ba domin yana bin umarnin na sama dashi ne. Yace kuma jami'an gwamnati su guji wulakanta sojoji dan yin hakan kamar wulakanta shugaban kasa ne. Yace Wike bai kamata ace yayi ja in ja da matashin sojan ba, kamata yayi ace ya nemi manyan sojan yayi magana dasu. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a DCL Hausa.
Kalli Bidiyo: A gidana kowa abinci kala daya yake ci, Tun daga Megadi, Direba har ni duk kalar abincin dana ci shi zasu ci>>Inji Shahararren Mawakin, Davido

Kalli Bidiyo: A gidana kowa abinci kala daya yake ci, Tun daga Megadi, Direba har ni duk kalar abincin dana ci shi zasu ci>>Inji Shahararren Mawakin, Davido

Duk Labarai
Shahararren Mawakin Najeriya, Davido ya bayyana cewa duk kalar abincin daya ci, shine Direbansa da kowa da kowa yake ci a gidansa. Ya bayyana cewa, matarsa na tabbatar da hakan inda yace irin tarbiyyar da aka masa a gidansu kenan. Davido wanda mahaifinsa shahararren me kudine yace a baya babu wanda yasan mahaifinsa duk da yana da kudi amma da ya fara wakane ya rika fadin irin abinda mahaifinsa ya mallaka mutane suka fara sanin wanene mahaifinsa. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi. https://www.tiktok.com/@boyjulian.22/video/7571427066902564152?_t=ZS-91MTYhXyKzg&_r=1
Da Duminsa: Gwamnati tasa a yi abincike kan takaddamar data faru tsakanin Ministan Abuja, Nyesom Wike da soja A. Yerina

Da Duminsa: Gwamnati tasa a yi abincike kan takaddamar data faru tsakanin Ministan Abuja, Nyesom Wike da soja A. Yerina

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Ministan Tsaro, Muhammad Badaru yasa a gudanar da bincike kan takaddamar data faru tsakanin Ministan Abuja, Nyesom Wike da sojan Ruwa, A. Yerima. Saidai Ministan yace zasu tabbatar duk sojan dake bakim aikinshi yayi aikinshi da kyau an bashi goyon baya da kariya. Ya jinjinawa soja Yerima bisa kwarewar aiki da ya nuna a yayin takaddamarsa da Nyesom Wike.