Tuesday, December 16
Shadow
Yanda Sanata Akpabio Ya taba rike hannuna a gaban mijina>>Sanata Natasha Akpoti

Yanda Sanata Akpabio Ya taba rike hannuna a gaban mijina>>Sanata Natasha Akpoti

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti daga jihar Kogi ta bayar da labarin yanda Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ya taba rike hannunta a gaban mijinta. Tace a lokacin sun je taya Akpabio murnar zagayowar ranar haihuwarsa ne inda mijinta ya rakata. Tace Sanata Akpabio ya kama hannunta ya jata ya rika nuna mata gidansa yayin da mijinta ke binsu a baya. Tace abin ya damu mijinta a lokacin wanda daga nan ya rika cewa ba zata rika yin tafiya ita kadai ba.
GWAMNATIN JIHAR KEBBI TA AURARDA ‘YA’YA MATA 300 (DA MAZAJENSU) KARO NA 2 !

GWAMNATIN JIHAR KEBBI TA AURARDA ‘YA’YA MATA 300 (DA MAZAJENSU) KARO NA 2 !

Duk Labarai
A jiya Alhamis ne (27/02/2025) Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin zababben Gwamnan Jihar (Comr. Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu) ta sake daurawa mata 300 aure da mazajensu , tareda duk abinda ya dace ayi musu na karramawa (auren gata kenan). Wannan kudurin (na shirin auren gata) mai girma Gwamnan Jihar Kebbi ya sanya shi a ransa , cewa da ikon Allah zai yi iya na shi kokari don ganin gwamnatinsa ta ci gaba da bada irin wannan gudummuwa musamman ga marasa karfi , don taimakawa al'umma wajen rage yawan gwagware da kuma rage yaduwar alfasha a cikin al'umma. Ko shakka babu wannan ba karamin alkhairi bane a cikin al'umma musamman idan sun gano hadarin da ke cikin yawaitar mabukata aure mata/maza kuma ba suda halin yin auren , a irin wannan lokacin komai na iya faruwa a kowane bangar...
Tonon Silili: Dama can Sanata Akpabio da Natasha Akpoti sun san juna kamin ta zama sanata>>Inji Daya daga cikin sanatocin

Tonon Silili: Dama can Sanata Akpabio da Natasha Akpoti sun san juna kamin ta zama sanata>>Inji Daya daga cikin sanatocin

Duk Labarai
Sanata me wakiltar Birnin Tarayya, Ireti Kingibe ta bayyana cewa dama can sanata Natasha Akpoti da kakakin majalisar, Godswill Akpabio sun san juna kuma akwai wani abu a tsakaninsu kamin ta zama sanata. Ta bayyana hakane a yayin da sanata Natasha Akpoti ta fito ta zargi kakakin majalisar da cewa ya nemeta da lalata ne ta ki shiyasa ya canja mata gurin zama a majalisar kuma yake dakile kudirorin da take kawowa. Sanata Ireti Kingibe ta bayyana cewa, ba Sanata Natasha Akpoti kadai bace aka canjawa wajan zama a ranar ba. Ta jawo hankalin cewa hakan tsari ne na majalisar wanda kuma duk dan majalisar ya kamata yana girmama hakan.
Da Duminsa:An dauke wutar Lantarki a fadar shugaban kasa, Tinubu

Da Duminsa:An dauke wutar Lantarki a fadar shugaban kasa, Tinubu

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban Najeriya dake Abuja sun bayyana cewa an samu daukewar wutar lantarki. Matsalar wutar lantarkin ta farune a wasu sassan na Abuja wanda har ta kai ga lamarin ya taba fadar shugaban kasar. Hukumar wutar lantarki ta Abuja, (AEDC) ta tabbatar da hakan a shafinta na X inda ta baiwa masu hulda da ita hakuri da kuma tabbacin cewa injiniyoyinta na aiki tukuru dan shawo kan matsalar. Karin guraren da matsalar wutar lantarkin suka shafa sun hada da Lugbe da Kubwa.
MASHA ALLAH: Kalli Hotunan Yadda Aka Kawata Masallacin Sheik Yusuf Guruntum Domin Fuskantar Tafsirin Watan Ramadan.

MASHA ALLAH: Kalli Hotunan Yadda Aka Kawata Masallacin Sheik Yusuf Guruntum Domin Fuskantar Tafsirin Watan Ramadan.

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} MASHA ALLAH: Yadda Aka Kawata Masallacin Sheik Yusuf Guruntum Domin Fuskantar Tafsirin Watan Ramadan.
Da Mahaifiyata ta mutu, An bani Kyautar Naira Miliyan dari biyar amma naki karba dan tsare mutunci na>>Inji Shugaban EFCC

Da Mahaifiyata ta mutu, An bani Kyautar Naira Miliyan dari biyar amma naki karba dan tsare mutunci na>>Inji Shugaban EFCC

Duk Labarai
Shugaban hukumar EFCC dake yaki da rashawa da cin hanci a Najeriya, Olanipekun Olukoyede yace a shekarar 2019 mahaifiyarsa ta rasu. Yace ana kwana daya za'a binneta ya je gida dan halartar jana'izarta. Yace akwai gidansa da ya gina tun kamin ya fara aiki da EFCC kuma a wancan lokacin yana mukamin sakatarene a hukumar, yace yana zuwa gida sai ya tarar da shanu an kawo masa. Yace sannan kuma ya tarar da me gadinsa ya bashi wani akwati cike da Check na banki. Yace da ya shiga gida sai matarsa ta daga hannu sama tace sun godewa Allah, amma anan ya taka mata birki, yace nan suka zauna suka duba duka kudaden da aka aika masa wanda sun kai Naira Miliyan 500. Yace wadanda suka aika masa da wadanna kudade manyan ma'aikata ne da ministoci a ma'aikatun da suke bincike. Yace a sheka...
Kalli Hotunan yanda akawa wasu ‘yan luwadi da aka kama bulala 80 kowannensu a kasar Indonesia

Kalli Hotunan yanda akawa wasu ‘yan luwadi da aka kama bulala 80 kowannensu a kasar Indonesia

Duk Labarai
Kasar Indonesia ta zane wasu mutane maza 2 da aka kama suna aikata Luwadi. an zane su ne a gaban gwamman Mutane dan ya zama izina ga meyi ya daina. An yi wannan bulala ne a yankin Aceh na kasar a ranar Alhamis. Shi wannan yanki na Aceh ya kasance yana aiki ne da shari'ar Musulunci. Tun a watan Nuwamba da ya gabata ne mutane suka kamasu turmi da tabarya wanda daga nan ne suka kaisu kotun shari'ar Musulunci.
Za a ƙara alawus ɗin abinci na sojojin Najeriya zuwa naira 3,000

Za a ƙara alawus ɗin abinci na sojojin Najeriya zuwa naira 3,000

Duk Labarai
Babban hafsan sojin ƙasan Najeriya, Laftanar janar Olufemi Oluyede ya bayyana rashin jin daɗinsa kan kuɗin alawus na kullum da ake RCA da ake ba sojojin Najeriya, wanda yanzu ake ba su naira 1,500. Da yake yi wa sojojin sashe na 81 jawabi a Legas, Oluyede ya ce za a ƙara alawus ɗin zuwa naira 3,000 daga wata mai zuwa. Baya ga ƙarin na RCA, babban hafsan ya ce rundunar sojin ƙasan Najeriya za ta fara ba sojoji lamunin kuɗi a kan kuɗin ruwa na kashi 3, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito. Ya ba sojoji shawarar su nemi bashin kuɗin, domin a cewarsa biyan ba zai zama musu matsala saboda babu ruwa mai girma a ciki. A game da tsarin gidaje, janar ɗin ya ce za su faɗaɗa shirirnsu na lamunin gidaje a Abuja da Ibadan da Jos da Fatakwal da Owerri da Akwa Ibom. Ya ce a tsarin,...
Sarkin Musulmin Najeriya ya buƙaci a fara duba watan Azumi daga gobe Juma’a

Sarkin Musulmin Najeriya ya buƙaci a fara duba watan Azumi daga gobe Juma’a

Duk Labarai
Mai alfarma sarkin Musulmin Najeriya, Muhamad Sa'ad Abubakar III na sanar da fara duba watan Ramadan daga gobe Juma'a 28 ga watan Sha'aban, wanda ya yi dai dai da 29 ga watan Janairun 2025. Cikin wata sanarwa da shugban kwamitin harkokin addini na fadar mai Alfarmar, Farfesa Sambo Wali Junaidu ya fitar ranar Alhamis ya ce idan aka ga watan a sanar da fadar mai alfarmar ta hanyar wasu lambobin waya da ya bayar. Sanarwar ta ƙara da cewa idan ba a ga watan a ranar Juma'a ba, to ranar Lahadi za ta kasance 1 ga watan Ramadan na wannan shekara. A ranar Laraba ne dai hukumomin Saudiyya suka da fara duba watan Ramadan ɗin daga gobe Juma'ar.