Hisbah ta fara kwashe yaran da ke gararamba kan titunan Kano
Gwamnatin Kano ta fara kwashe 'dubban' yara da ke rayuwa a kasuwanni da ƙasan gadoji a Kano, babban birnin jihar.
Gwamnatin ta fara ɗaukar matakin ne a jiya Litinin, inda ta samar da wani sansanin ajiyewa da kuma tantance yaran.
Shugaban hukumar Hisbah a jihar, Sheikh Aminu Daurawa ya ce "mun samu rahoton akwai ɗaruruwa ko kuma dubban ƙananan yara da ba su haura shekara 15 ba waɗanda suke kwana a ƙarƙashin gadoji da cikin tashoshi da kuma kasuwanni."
"Ci gaba da rayuwarsa a waɗannan wurare zai iya haifar da matsala ta tsaro da ta zamantakewa a nan gaba," in ji Daurawa.
Shugaban na hukumar Hizba ya ce alƙaluman da suke da su sun nuna cewa akwai irin waɗannan yara masu gararamba a kan tituna sama da 5000.
Ya kuma bayyana cewa za a tara yaran da aka kwashe ne a wata cibiya, ind...








