Tuesday, December 16
Shadow
Hisbah ta fara kwashe yaran da ke gararamba kan titunan Kano

Hisbah ta fara kwashe yaran da ke gararamba kan titunan Kano

Duk Labarai
Gwamnatin Kano ta fara kwashe 'dubban' yara da ke rayuwa a kasuwanni da ƙasan gadoji a Kano, babban birnin jihar. Gwamnatin ta fara ɗaukar matakin ne a jiya Litinin, inda ta samar da wani sansanin ajiyewa da kuma tantance yaran. Shugaban hukumar Hisbah a jihar, Sheikh Aminu Daurawa ya ce "mun samu rahoton akwai ɗaruruwa ko kuma dubban ƙananan yara da ba su haura shekara 15 ba waɗanda suke kwana a ƙarƙashin gadoji da cikin tashoshi da kuma kasuwanni." "Ci gaba da rayuwarsa a waɗannan wurare zai iya haifar da matsala ta tsaro da ta zamantakewa a nan gaba," in ji Daurawa. Shugaban na hukumar Hizba ya ce alƙaluman da suke da su sun nuna cewa akwai irin waɗannan yara masu gararamba a kan tituna sama da 5000. Ya kuma bayyana cewa za a tara yaran da aka kwashe ne a wata cibiya, ind...
Tinubu na cikin mutanen da suka fi tsara manyan laifuka da rashawa a 2024 – OCCRP

Tinubu na cikin mutanen da suka fi tsara manyan laifuka da rashawa a 2024 – OCCRP

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu na cikin na gaba-gaba a jerinn mutanen da suka fi tsara manyan laifuka da kuma aikata cin hanci da rashawa, a cewar rahoton cibiyar kula da aikata manyan laifuka da rashawa ta duniya. CIbiyar Organized Crime and Corruption Reporting Project (OCCRP) kan nemi 'yanjarida da ƙwararru da ɗaiɗaikun mutane su kaɗa ƙuri'a wajen zaɓen mutanen da suka fi aikata tsararrun laifkuka a ɓangaren cin hanci da rashawa duk shekara. Tinubu ne ya zo na uku a jerin, yayin da tsohon Shugaban Syria Bashar al-Assad ya zo na ɗaya "saboda abubuwan da suka faru a ƙasar a baya-bayan nan," in ji OCCRP. Sai dai zuwa yanzu gwamnatin Najeriya ko Tinubu kansa ba su ce komai ba game da sakamakon ƙuri'ar. Duk da cewa shi ne ya fi kowa yawan ƙuri'u, Shugaban Kenya William Ruto n...
Ka daina karya saboda ka kai shekaru 80>>Kwankwaso ya gayawa Atiku

Ka daina karya saboda ka kai shekaru 80>>Kwankwaso ya gayawa Atiku

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa, bai kamata mutane da suka kai shekaru 70 zuwa 80 ba su rika karya. Ya bayyana hakane a matsayin martani ga maganar Atiku Abubakar ta cewa sun hada kai dan kwace mulki daga hannun APC a shekarar 2027. Kwankwaso ya bayyana cewa wannan magana bai san da ita ba kuma jinta ya bata masa rai. Yace wannan ne matsalar Najeriya. ya kara da cewa, Jam'iyyar PDP ta mutu ne shiyasa take nema sai ta hada kai da wasu jam'iyyun kamin ta samu nasarar karbar Mulki.
Hoto: An kama wani mutum da muggan makamai a Abuja

Hoto: An kama wani mutum da muggan makamai a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja sun bayyana cewa, An kama wani mutum da muggan makamai a birnin tarayyar. Mutumin me suna, Obinna Nwigwe An kamashi ne bayan samun bayanan sirri daga Najob Guest House dake Bwari. A yayin da jami'an tsaro suka je kamashi, an iskeshi ya harbi wani mutum bayan da suka yi gaddama. Bincike da aka yi sosai a gidansa an gano karin makamai da Albarusai. wanda ya harba din, Andrew Philemonna can Asibiti yana jinya, a yayin da shi kuma ake bincike akansa.
Hotuna: Wani muatashi ya kkashe mahaifiyarsa ya jefa gawar a cikin rijiya

Hotuna: Wani muatashi ya kkashe mahaifiyarsa ya jefa gawar a cikin rijiya

Duk Labarai
Ana zargin wani matashi da kashe mahaifiyarsa sannan ya jefa gawarta a cikin rijiya a Jihar Cross River. Lamarin ya farune ranar Lahadi a titin Chairman Road, dake garin Ohong karashin karamar hukumar Obudu na jihar. A wani bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook, an ga yanda mutanen unguwa suka taru ake zaro gawar matar daga rijiyar da dan nata ya jefata. Rahotanni sunce wani abokinsa ne ya taimaka masa wajan gudanar da wannan danyen aikin. Ya yiwa 'yar aikin gidansu baranar cewa idan ta sake ta gayawa wani sai ya kasheta. Ya dauki yarinyar aikin gidan nasu akan mashin zuwa wani wajene inda akan hanya 'yan Bijilante suka taresu, anan ne Asirinsa ya tonu.
An min Wahayi cewa, za’a yi yunkurin kkashe shugaban kasa ta hanyar bashi guba amma zai tsallake, sannan wani gwamna zai muttu a 2025>>Inji Fasto Ayodele

An min Wahayi cewa, za’a yi yunkurin kkashe shugaban kasa ta hanyar bashi guba amma zai tsallake, sannan wani gwamna zai muttu a 2025>>Inji Fasto Ayodele

Duk Labarai
Babban fasto, Primate Ayodele ya bayyana abubuwan da zasu faru a shekarar 2025 kamar yanda ya saba yi duk shekara inda yake ikirarin an masa wahayi. Faston yace wasu daga cikin abubuwan da aka masa wahayi shine cewa za'a saki shugaban kungiyar IPOB dake son kafa kasar Biafra watau, Nnamdi Kanu, sannan matsin rayuwa zai karu a shekarar ta 2025. Yace ya kuma gano cewa wani gwamna zai mutu, sannan za'a yi yunkurin kashe wani shugaban kasa ta hanyar zuba masa guba amma zai tsallake, saidai be bayyana kowane shugaban kasa bane. Ya kuma za'a samu matsalar kisan jami'an tsaro na FBI da CIA na kasar Amurka.