Lauyoyin Jihar Zamfara Sun Goyi Bayan Gayyatar Gwamna Dauda A Gaban Majalisa Kan Ŕikicin Majalisar Ďokoki
Lauyoyin Jihar Zamfara Sun Goyi Bayan Gayyatar Gwamna Dauda A Gaban Majalisa Kan Ŕikicin Majalisar Ďokoki.
Kungiyar lauyoyin Jihar Zamfara ta bayyana goyon bayanta ga matakin da Majalisar Wakilai ta Nijeriya ta dauka na gayyatar Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, da shugabannin majalisar dokokin jihar domin su bayyana kan rikicin da ke kara tsananta a majalisar dokokin jihar da kuma tabarbarewar tsaro a fadin jihar da ke arewa maso yammacin Nijeriya.
Wannan kungiya, wadda ke da matsayi a fannin kare doka da tsarin mulki, ta bayyana kiran a matsayin matakin da kundin tsarin mulki ya amince da shi, bisa tanade-tanaden sashe na 88 da 89 na Kundin Tsarin Mulki na 1999, wanda ya ba Majalisar Tarayya damar gudanar da bincike kan batutuwan da suka shafi jama’a da kuma kiran jami’ai mas...








