Saturday, December 20
Shadow
‘Yan majalisar tarayya dake jam’iyyun Adawa sun nemi Gwamnati data biya ma’aikata Naira Dubu dari(100,000) a matsayin mafi karancin Albashi

‘Yan majalisar tarayya dake jam’iyyun Adawa sun nemi Gwamnati data biya ma’aikata Naira Dubu dari(100,000) a matsayin mafi karancin Albashi

Siyasa
'Yan majalisar tarayya dake jam'iyyun Adawa irin su PDP, Labour party da sauransu, sun yi kiran cewa, ya kamata gwamnati ta biya ma'aikata Naira dubu 100 a matsayin mafi karancin Albashi. Shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda ne ya bayyana hakan a hirar da aka yi dashi a gidan jaridar Punch. Yace a halin da ake yanzu, duk albashin da za'a biya dake kasa da Naira 298,000 ba zai kai ma'aikaci ko ina ba. Ya kara da cewa, kasa biyan albashin da zai ishi ma'ikata yin rayuwa me kyau, sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya ne.
Kungiyar Kwadago ta sauko daga dubu dari hudu(400,000) yanzu tace zata amince idan gwamnati ta biya dubu dari(100,000) a matsayin mafi karancin Albashi

Kungiyar Kwadago ta sauko daga dubu dari hudu(400,000) yanzu tace zata amince idan gwamnati ta biya dubu dari(100,000) a matsayin mafi karancin Albashi

Siyasa
Kungiyar kwadago ta NLC ta dauko daga matsayinta na sai gwamnati ta biyata dubu dari hudu da casa'in da hudu(494,000) a matsayin mafi karancin Albashi. A yanzu kungiyar tace zata iya amincewa da dubu dari(100,000) a matsayin mafi karancin Albashi idan gwamnati zata iya biyan hakan. Hakan ya bayyana ne daga bakin wasu 'yan kungiyar wanda basuso a bayyana sunayensu ba. A zama na karshe dai da gwamnati ta yi da 'yan kwadagon ta ce zata biya Naira dubu sittin a matsayin mafi karancin albashi saidai kungiyar kwadagon tace bata amince ba. Labari na karshe dai shine wanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa ministan kudi, Wale Edun umarnin ya gabatar masa da sabin daftari na biyan ma'aikatan mafi karancin Albashi.
Hotuna: Dan Gidan Sheik Dahiru Bauchi Ya Ziyarci Sarki Aminu Ado Bayero Tare Da Ba Shi Kyautar Alkyabba Da Carbi

Hotuna: Dan Gidan Sheik Dahiru Bauchi Ya Ziyarci Sarki Aminu Ado Bayero Tare Da Ba Shi Kyautar Alkyabba Da Carbi

Kano
Dan Gidan Sheik Dahiru Bauchi Ya Ziyarci Sarki Aminu Ado Bayero Tare Da Ba Shi Kyautar Alkyabba Da Carbi. Sayyadi Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi ya kaiwa Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero ziyara tare da yi masa kyautar Alkyabba da carbi a yammacin yau a fadar shi dake Nasarawa. A yayin ziyarar yaja hankalin alumar Jihar Kano dasu zauna lafiya su bi doka, yakuma wuce zuwa hubbare domin yiwa Iyaye addua da ke kwance. Mai Martaba Sarki Alh. Aminu Ado Bayero ya bayyana jin dadin ziyarar girmamawar ya kuma godewa tawagar Sayyadi da kuma aiken gaisuwa ga Sheikh Dahiru Usman Bauchi da addu'ar Allah Ya kara masa lafiya da nisan kwana. Daga Abdulwahab Sa'id Ahmad
Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan kuɗi, Wale Edun, da ya fito da abubuwan da za a kashe akan sabon mafi ƙarancin albashi cikin kwanaki biyu

Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan kuɗi, Wale Edun, da ya fito da abubuwan da za a kashe akan sabon mafi ƙarancin albashi cikin kwanaki biyu

Siyasa
Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan kuɗi, Wale Edun, da ya fito da abubuwan da za a kashe akan sabon mafi ƙarancin albashi cikin kwanaki biyu. Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na ƙasa, Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban ƙasa bayan wata ganawar da tawagar ta yi da shugaban ƙasar a Aso Rock Villa, a ranar Talata.
WATA SABUWA: Babu Wanda Muka Yi Wa Mubaya’a Tsakanin Sarki Sanusi II Da Sarki Aminu Ado Bayero, Cewar Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi

WATA SABUWA: Babu Wanda Muka Yi Wa Mubaya’a Tsakanin Sarki Sanusi II Da Sarki Aminu Ado Bayero, Cewar Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi

Kano
WATA SABUWA: Babu Wanda Muka Yi Wa Mubaya'a Tsakanin Sarki Sanusi II Da Sarki Aminu Ado Bayero, Cewar Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi Sayyadi Muktar Ibrahim Dahiru Bauchi ya musanta labarin da wasu jaridu suka wallafa cewar sun je sun yi wa Sarki Sunusi II mubaya'a sannan suka kara yi wa Sarki Aminu Ado Bayero mubaya'a. A cewar sa sun kai ziyarar ne karkashin wata kungiya da Sheikh Aminu Dahiru Bauchi ke jagoranta na hadin kan al'umma musulmi tare da samar da cigaba, inda daga nan suka kuma kaiwa Sarki Aminu ziyara domin jajantawa akan abun da ya faru da shi. "Mu ba mu dauki bangare ba, kawai muna fatan Allah ya kawo dauki ne akan abun da ke faruwa a Kano, domin duk wani Musulmi a Arewa ba zai ji dadin abun da ke faruwa ba a Gidan Dabo", inji SayyadiMukhtar Ibrahim Sheik Dahiru Ba...
Ba zamu amince da kari dan kadan ba akan Dubu 60>>NLC

Ba zamu amince da kari dan kadan ba akan Dubu 60>>NLC

Siyasa
Kungiyar Kwadago ta NLC ta bayyana cewa, ba zata amince da kari dan kadan, wanda bai kai ya kawo ba akan Naira Dubu 60 ba. Kungiyar Kwadago ta NLC dai ta amince ta dakatar da yajin aikin da take dan bayar da dama ga gwamnati ta mata kari akan Naira Dubu 60 na mafi karancin Albashi. Shugaban kungiyar Kwadago ta TUC, Festus Osifo ne ya bayyana haka a wata ganawa da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Yace su basu nace wai sai an biyasu Naira Dubu dari hudu ba amma dai abinda suke cewa, shine a biyasu albashi me kyau.
Mun kunno wutar lantarki bayan janye yajin aiki – Ma’aikatan lantarki a Najeriya

Mun kunno wutar lantarki bayan janye yajin aiki – Ma’aikatan lantarki a Najeriya

Duk Labarai
Ƙungiyar ma'aikatan wutar lantarki ta ƙasa a Najeriya ta ce an sake kunna babban layin wutar da aka kashe bayan janye yajin aikin da ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC suka yi.Shugaban ƙungiyar National Union of Electricity Employees (NUEE), Adebiyi Adeyeye, ya faɗa wa jaridar Punch cewa sun kunna layin ne bayan janye yajin aikin a safiyar yau."An janye yajin aiki kuma hakan yana nufin layin ya koma aiki yadda ya dace. An kunna shi tuni," in ji Mista Adeyeye.Sai dai har yanzu akasarin ƙasar na cikin duhu duk da wannan iƙirari da shugaban ya yi.Tun a jiya Litinin kamfanin kula da rarraba lantarki a Najeriya TCN ya ce mambobin ƙungiyar ƙwadago ne suka tilasta wa ma'aikatan lantarkin shiga yajin aikin ta hanyar kashe babban layin.