Kalli Bidiyo: NLC ta kulle jami’ar Kaduna Polytechnic
Kungiyar kwadago ta NLC reshen jihar Kaduna ta kulle jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kaduna Polytechnic biyo bayan yajin aikin data fara a yau, Litinin na sai baba ta gani.
NLC sun je reshen jami'ar dake Unguwan Rimi inda suka fitar da daliban dake ciki suka kulle makarantar, kamar yanda Channels TV ta ruwaito.
https://twitter.com/channelstv/status/1797559071605653659?t=47Z-RGNiOLuG4lJF6Zot5Q&s=19
A Abuja ma dai haka lamarin yake inda NLC ta kulle guraren aiki da yawa ta hana ma'ikata shiga.








