
Wasu Rahotanni sun bayyana cewa, Aliko Dangote na shirin fara sayar da duka man da ya tace a matatarsa zuwa kasashen waje.
Rahoton yace Dangote na fushi ne da Gwamnatin Najeriya saboda har yanzu tana baiwa ‘yan kasuwa lasisin shigowa da man fetur duk da yake cewa ga matatar mansa tana samar da man.
Kasashen Afrika irin su Afrika ta Kudu da sauransu na yiwa Dangote matsin lamba kan ya kara yawan man fetur din da yake sayar musu.