Thursday, February 26
Shadow

Sanata Natasha Akpoti ta dauko dala ba Gammo inda ta kai karar Sanata Godswill Akpabio majalisar Dinkin Duniya acan ma ta masa tonon silili da terere

Sanata Natasha Akpoti da majalisar dattijai ta dakatar saboda zargin karya dokar majalisar ga dukkan alamu bata hakura ba.

A wani taron mata ‘yan majalisa na Duniya da aka yi a majalisar Dinkin Duniya dake birnin New York na kasar Amurka, Sanata Natasha Akpoti a can ma ta taso da maganar dakatar da ita.

Tace an mata rashin adalci da take hakkinta, inda tace akwai yiyuwar ma a tsareta a birnin New York.

Ta bayyana cewa, tana fargabar tana cikin matsalar tsaro.

Karanta Wannan  Bidiyo Da Duminsa: Hukumomin Gwamnatin Soji ta kasar Burkina Faso sun ce auna rike da sojojin Najeriya 11 bayan da jirginsu yayi saukar gaggawa a kasar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *