
Masu Laifi dake daure a gidan gyara hali na garin Jos a jihar Filato sun koka da cewa, yanayin da suke ciki ya munana.
A wani rahoto da kafar Sahara reporters ta wallafa, mai laifin sunce shekara daya kenan rabonsu da cin nama ko kifi, sai wake wanda babu wani abun gina jiki a cikinsa.
Hakanan sun koka da cewa, idan basu da lafiya babu kulawa kuma ana azabtar dashi ga nuna kabilanci.
A wani hoto da aka wallafa, an ga kalar abincin da ake baiwa masu laifin wanda ya hada da wake da garin rogo da miyar Kuka.