Tuesday, February 24
Shadow

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna, Gobe Juma’a

Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna a gobe, Juma’a idan Allah ya kaimu.

Shugaban zai halarci daurin auren dan Sanata Abdulaziz Yari me suna Nasirudeen Yari da amaryarsa, Safiyya Shehu Idris.

Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa da me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar 18 ga watan Satumba.

Hakanan sanarwar tace shugaban kasar zai kuma kaiwa matar tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari ziyara.

Sannan a Ranar Juma’ar dai ne shugaban zai koma Abuja.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon sojan da ya Tona Asirin sojojin da suka yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki, kuma ya dakilesu, har An kara masa mukami zuwa Lt-Gen

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *