
Wata hatsaniya ta faru a Cocin Redeem church dake Karu a babban birnin tarayya, Abuja bayan da aka zargi faston cocin da dirkawa daya daga cikin membobinsa ciki.
Rahoton yace faston ya zubar da cikin bayan da ya ga Asirinsa zai tonu.
Sannan ya bayar da Naira miliyan 3 toshiyar baki dan kada a tona masa asiri amma duk da haka ana tsaka da taron Lahadi a cocin wani ya masa tonon silili.