Thursday, December 25
Shadow

Trump bai isa ya Hana Aiki da shari’ar Musulunci a Jihohin Arewa ba>>Inji Kungiyar Dattawan Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa, NEF ta mayarwa da shugaban kasar Amirka, Donald Trump da martani me zafi inda tace shugaban Amurkar, Trump bai isa ya hana aiki da Shari’ar Musulunci a Jihohin arewa ba

Wasu daga cikin ‘yan majalisar kasar Amurka da wasu kungiyoyin fafutuka a kasar sun nuna damuwa kan amfani da shari’ar Musulunci a jihohin Arewa.

Dan haka suke kiran a daina amfani da shari’ar Musulunci a Arewa sannan a sakawa wasu jami’an gwamnatin Najeriya takunkumi.

Saidai kungiyar NEF ta bakin me magana da yawunta, Prof Abubakar Jiddere tace babu wannan maganar, Trump girman kai ne ke Damunsa kuma barzanar da yake yi ta banza da wofi ce babu abinda zai iya.

Karanta Wannan  Sanata Natasha Akpoti ta dauko dala ba Gammo inda ta kai karar Sanata Godswill Akpabio majalisar Dinkin Duniya acan ma ta masa tonon silili da terere

Sannan kungiyar tace babu maganar yiwa Kiristoci Khisan Kyiyashi a Arewa matsalar tsaro tana shafar kowa da kowane.

Hakanan itama gamayyar Kungiyoyin fafutuka na arewa, The National Coordinator of the Coalition of Northern Groups ta bakin shugabanta, Jamilu Aliyu Charanchi, tace wannan abu zai karawa mutane tsanar kasashen yamma ne kawai.

Yace Shari’ar Musulunci ba wai doka bace kawai, abune wanda ‘yan Arewa musulmi suka yadda cewa daga Allah ne kuma haka rayuwarsu ya kamata ta kasance.

Yayi gargadin cewa, duk Gwamnan da ya sake yayi yunkurin sassautawa ko cire shari’ar Musulunci to zai fuskanci kakkausan Martani daga Al’ummar Arewa da malamai.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon da Duminsa: Yanda Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja, FCDA karkashin Wike ta kutsa da karfi cikin Ginin River Park duk da Umarnin Kotu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *