Friday, December 5
Shadow

Yanzu-Yanzu: Ganduje ya bayyana ainahin dalilin da yasa ya sauka daga shugaban APC

Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga shugabancin jam’iyyar APC a yau, Juma’a.

Ya bayyana hakane a wata wasika da ya aikewa jam’iyyar. A cikin wasikar, Ganduje ya bayyana dalilin rashin lafiya a matsayin abinda yasa ya sauka daga mukamin nasa.

Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya sha suka daga mutanen yankin Arewa maso gabas saboda zargin rashin goyon bayan Kashim Shettima a matsayin abokin takarar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027 me zuwa.

An bayyana cewa wani daga cikin mataimakan Gandujenne zai zama shugaban riko na jam’iyyar kamin babban zabenta a watan Disamba me zuwa.

Karanta Wannan  Majalisar Koli ta addinin Musulunci a Najeriya tace Babu Mhuzghunawar da akewa Kiristoci saidai Kungiyar Kiristoci ta PFN tace da gaske ana Mhuzghuna musu kuma hakurinsu ya kusa karewa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *