Friday, June 26
Shadow

Yanzu-Yanzu: Ganduje ya bayyana ainahin dalilin da yasa ya sauka daga shugaban APC

Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga shugabancin jam’iyyar APC a yau, Juma’a.

Ya bayyana hakane a wata wasika da ya aikewa jam’iyyar. A cikin wasikar, Ganduje ya bayyana dalilin rashin lafiya a matsayin abinda yasa ya sauka daga mukamin nasa.

Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya sha suka daga mutanen yankin Arewa maso gabas saboda zargin rashin goyon bayan Kashim Shettima a matsayin abokin takarar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027 me zuwa.

An bayyana cewa wani daga cikin mataimakan Gandujenne zai zama shugaban riko na jam’iyyar kamin babban zabenta a watan Disamba me zuwa.

Karanta Wannan  Mijinta ya kamata tana yiwa dan kishiyarta me shekaru 15 fyade, saidai duk da haka ta sake kiran yaron inda take tambayarshi ta gamsar dashi kuwa?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *