EFCC Ta Yi Alkawarin Bincikar Matawalle akan zargin wawure sama da Naira biliyan 528.

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta yi alkawarin gudanar da bincike kan zargin karkatar da kudi da aka yi wa Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, biyo bayan wani koke da jam’iyyar All Progressives Congress Young Leaders Alliance (APC-YLA) ta gabatar.
Zarge-zargen dai na zargin Matawalle da wawure sama da Naira biliyan 528 a lokacin da yake Gwamnan Jihar Zamfara.
Wannan tabbacin ya zo ne a wata zanga-zangar da aka gudanar ranar Juma’a a hedikwatar EFCC da ke Abuja, inda shugaban jam’iyyar APC-YLA Convener, Mohammed Ireji, da sauran masu zanga-zangar suka bukaci a sake bude shari’ar cin hanci da rashawa da ake yi wa Matawalle.
Ireji ya nuna shakku kan jinkirin da aka samu wajen binciken tsohon gwamnan, inda ya bayar da misali da koke-koken da aka gabatar a baya ga EFCC, ciki har da na APC Akida Forum a ranar 3 ga Mayu, 2024, da kuma bin diddigin ranar 30 ga Satumba, 2024.
Da yake karbar koken, mukaddashin daraktan tsaro na EFCC, Idowu Adedeji, ya ce, “Mun karbi koken ku, kuma za mu gabatar da shi a kan haka.”
Daga Mikiya.