Monday, May 12
Shadow
Rashin Tabbas bayan kammala karatu da tsadar Rayuwa tasa yanzu iyaye sun fara tura ‘ya’yansu koyan aikin hannu

Rashin Tabbas bayan kammala karatu da tsadar Rayuwa tasa yanzu iyaye sun fara tura ‘ya’yansu koyan aikin hannu

Duk Labarai
Rahotanni sun ce iyaye a yanzu sun fara hakura da maganar sai 'ya'yansu sun samu aikin Gwamnati da daukar albashi me tsoka. Inda aka fara tura yara koyon sana'a yayin da suke zuwa makaranta a lokaci guda. Rahoton wanda jaridar Vanguard ta hada, yace yanzu yara tun daga shekara 10 ana fara turasu zuwa koyon aiki dan su dogara da kansu da kaucewa matsalar su kammala karatu ya zamana sun zauna babu aikin yi. Wasu kuma na tafiya da 'ya'yan nasu ne wajan aikin da suke dan su rika koya musu da wuri. Lamarin matsalar rashin aikin yi a tsakanin matasa ya zama ruwan dare inda dubbai sun kammala karatu amma basu samu aikin zama a ofis ba.
Duka da zagin me laifi baya cikin aikin ku>>Hukumar ‘Yansandan Najeriya ta gayawa ‘yansandan

Duka da zagin me laifi baya cikin aikin ku>>Hukumar ‘Yansandan Najeriya ta gayawa ‘yansandan

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan babban birnin tarayya, Abuja ta gargadi 'yansandan cewa duka da zagin wanda ake zargi baya cikin aikinsu. An bayyana musu hakane a yayin wani taron karawa juna Sani da aka yi. https://www.youtube.com/watch?v=Misftjbq4_A Akan samu rahotannin jikkata masu laifi ko wanda ake zargi da 'yansanda suka kama daga lokaci zuwa Lokaci.
Ziyarar Kakakin ‘yansandan Najeriya kasar Ingila ta jawo cece-kuce inda mutane ke tambayar ina ya samu kudin zuwa Ingila?

Ziyarar Kakakin ‘yansandan Najeriya kasar Ingila ta jawo cece-kuce inda mutane ke tambayar ina ya samu kudin zuwa Ingila?

Duk Labarai
Kakakin 'yansandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin ya je kasar Ingila ziyara. Ya wallafa hotunan ziyarar tasa inda yake daukar hotuna a gurare masu daukar hankali. https://twitter.com/BenHundeyin/status/1921144147219517667?t=YNzgqkNgR-RWLdv2uGz5gg&s=19 Saidai mutane da yawa na tambayar nawane Albashinsa da har ya iya zuwa kasar Ingila ziyara?
Ganduje zai dawo jam’iyyar mu ta PDP>>Inji Sule Lamido

Ganduje zai dawo jam’iyyar mu ta PDP>>Inji Sule Lamido

Duk Labarai
Jigo a jam'iyyar PDP tsohon gwamnan jihar Jigawa Alh.Sule Lamiɗo, ya yi hasashen cewa za a samu ɓarkewar rikici mai girma a jam'iyyar APC, inda ya ce nan da ɗa wani lokaci kaɗan jiga-jigai a Jam'iyyar APC, ciki har da shugaban jam'iyya na ƙasa, Dr.Abdullahi Umar Ganduje za su iya komowa cikin jam'iyyar PDP. Lamiɗo ya bayyana haka ne ya yin gangamin taron da aka gudanar a filin taro na Aminu kano Triangle a babban birinin jiha Dutse a lokacin zaɓan shuwagabannin jam'iyyar a matakin jiha. Ya ce "Na tabbatar da cewa waɗanda suka bar jam'iyyar PDP za su dawo, domin APC a cike take da rigima kuma nan ba da daɗewa ba gayyar za ta watse" ~Sule Lamiɗo Ya ƙara da cewa "Ku rubuta ku a jiy, nan da watanni shida da yawa daga cikin waɗanda suka koma j'iyyar APC za su dawo PDP, kuma idan suka y...
Karanta Jadawalin wanda suka halarci taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP

Karanta Jadawalin wanda suka halarci taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP

Duk Labarai
Ministan Tinubu na Abuja Nyesom Wike ya halarci taron jiga-jigan jam'iyyar PDP na Nijeriya da a ka gudanar a daren Lahadin a Abuja Taron wanda Gwamnan Bauchi Bala Mohammed ya kira da nufin Dinke Barakar da Jami’iyar PDP ke fama da ita ta samu halartar tsoffi da gwamnonin jam'iyyar PDP Da Shuwagabanin kamarMembers na National Working Committee (NWC) a jagoran Shugaban Riko Ambassador Iliya Damagum. GovernorH.E. Senator Bala Abdulkadir Mohammed (Bauchi State) - Chairman H.E Dr. Agbu Kefas ( Taraba State) - Member H.E. Rt. Hon. Ahmadu Umaru Fintiri (Adamawa State) - Member H.E. Dr. Dauda Lawal (Zamfara State) - Member H.E. Senator Ademola Adeleke, (Osun State) - Member H.E. Pastor Umo Eno Ph.D (Akwa Ibom State) - Member H.E. Dr. Peter Mbah (Enugu State) - Member H.E. B...
Nuna banbancin Addini ne da Muslim-Muslim da APC ta yi suka sa Peter Obi ya samu suna amma ba wai wani tsari me kyau gareshi ba>>Inji Omoyele Sowore

Nuna banbancin Addini ne da Muslim-Muslim da APC ta yi suka sa Peter Obi ya samu suna amma ba wai wani tsari me kyau gareshi ba>>Inji Omoyele Sowore

Duk Labarai
Mawallafin Jaridar Sahara Reporters kuma tsohon da takarar shugaban kasa a jam'iyyar AAC, Omoyele Sowore yace Peter Obi ya samu daukaka ne saboda nuna banbancin Addini. Ya bayyana cewa saboda APC ta tsayar da duka 'yan takara musulmai shiyasa Kirista su kuma suka zabi Peter Obi. Yace amma Peter Obi ba wani tsari ne gareshi da zai kawowa Najeriya ci gaba ba wanda za'a ce shine yasa shi ya samu daukaka.