
Yaran da ba’a haifa bane nake son baiwa Kariya shiyasa na cire tallafin Man fetur>>Tinubu
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, yaran da ba'a haifa nan gaba bane yake son ya baiwa kariya shiyasa ya cirw tallafin man fetur.
Shugaban ya bayyana hakane a fadarsa wajan kaddamar da kwamitin ci gaban matasa inda yace gwamnatinsa zata ci gaba da baiwa matasa kwarin gwiwa.
Shugaban yace idan ka duba masu karfafa cewa a bar Najeriya a tafi wata kasa ci rani, saboda babu ci gaba sosai, amma idan aka samu ci gaba, babu wanda zai so ya tafi wata kasar.
Shugaban yace a lokaci da ya fara mulki, matsaloli sun yi yawa inda ake ta kuka, yace amma yanzu tattalin arziki ya fara farfadowa inda farashin kayan masarufi ya sauka.