Tuesday, March 11
Shadow
Yaran da ba’a haifa bane nake son baiwa Kariya shiyasa na cire tallafin Man fetur>>Tinubu

Yaran da ba’a haifa bane nake son baiwa Kariya shiyasa na cire tallafin Man fetur>>Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, yaran da ba'a haifa nan gaba bane yake son ya baiwa kariya shiyasa ya cirw tallafin man fetur. Shugaban ya bayyana hakane a fadarsa wajan kaddamar da kwamitin ci gaban matasa inda yace gwamnatinsa zata ci gaba da baiwa matasa kwarin gwiwa. Shugaban yace idan ka duba masu karfafa cewa a bar Najeriya a tafi wata kasa ci rani, saboda babu ci gaba sosai, amma idan aka samu ci gaba, babu wanda zai so ya tafi wata kasar. Shugaban yace a lokaci da ya fara mulki, matsaloli sun yi yawa inda ake ta kuka, yace amma yanzu tattalin arziki ya fara farfadowa inda farashin kayan masarufi ya sauka.
Abubuwan da ya kamata ka sani game da komawar El-Rufai SDP

Abubuwan da ya kamata ka sani game da komawar El-Rufai SDP

Duk Labarai
A jiya ne tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana komawa Jam'iyyar SDP inda yace ya fita daga Jam'iyyar APC. A takardar barin APC da ya aikewa ofishin Jam'iyyar ya bayyana banbantar ra'ayi wanda yace ya gano ba zasu samu jituwa ba shi da Jam'iyyar ta APC. Yace a baya yana da niyyar saidai idan ya daina siyasa ne zai daina yin Jam'iyyar ta APC amma a yanzu saboda kaucewa tsari da banbancin ra'ayi, yace ya bar Jam'iyyar duk da yana daya daga cikin wanda suka kafata. El-Rufai yace babban abinda zai mayar da hankali a yanzu shine hado kan 'yan Adawa dan su hade su kayar da Jam'iyya me mulki zabe a shekarar 2027. Saidai a martanin da fadar shugaban kasa ta mayarwa da El-Rufai ta hannun ms baiwa shugaban kasar shawara a fannin sadarwa, Daniel Bwala yace zasu s...
Kalli bidiyon abinda Umar Bush yawa Dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da ake ta cece-kuce akai

Kalli bidiyon abinda Umar Bush yawa Dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da ake ta cece-kuce akai

Duk Labarai
Dan shugaban kasa, Seyi Tinubu a ziyarar da ya kai Kano ya hadu da shahararrun mutane da yawa ciki hadda me wasan barkwanci, Umar Bush. A wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta, An ga Seyi Tinubu ya zo wucewa inda Umar Bush ya zo ya gitta ta gabanshi. https://www.tiktok.com/@sirx_tik/video/7479756411438681399?_t=ZM-8uZOfsixc4E&_r=1 Lamarin ya baiwa mutane mamaki inda da yawa ke cewa bai damu da girman dan shugaban kasar ba.
Maganar Allah Kyan da sanata Natasha Akpoti ke dashi yayi yawa, shiyasa ba yadda za’a yi ta gitta namiji be kulata ba, dole ko da baka mata magana ba kadan kanne ido ko ka daga mata gira>>Sanata Adeseye Ogunlewe

Maganar Allah Kyan da sanata Natasha Akpoti ke dashi yayi yawa, shiyasa ba yadda za’a yi ta gitta namiji be kulata ba, dole ko da baka mata magana ba kadan kanne ido ko ka daga mata gira>>Sanata Adeseye Ogunlewe

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon Minista, Sanata Adeseye Ogunlewe ya bayyana cewa, Kyawun da Sanata Natasha Akpoti ke dashi shine babbar matsala a gareta. Ya bayyana hakane a yayin da ake hira dashi a gidan talabijin na Arise TV. Yace kyan da sanata Natasha Akpoti ke dashi, babu yanda za'a yi namiji me lafiya ya ganta ya kyale. Yace kuma su mata sanatoci suma suna magana da izza ta yanda baka isa kace musu mata ba, idan ka sake ma ka ce musu su mata ne zasu iya ganin kamar kana son ka rainasu ro za'a ...
Da Duminsa:APC ta gayawa Gwamna Fubara na jihar Rivers ko dai ya ajiye mukaminsa salin Alin ko a tsigeshi

Da Duminsa:APC ta gayawa Gwamna Fubara na jihar Rivers ko dai ya ajiye mukaminsa salin Alin ko a tsigeshi

Duk Labarai
Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Rivers, Tony Okocha ya baiwa gwamnan jihar, Siminalayi Fubara zabin ko dai ya ajiye mukaminsa salin Alin ko kuma a tsigeshi. Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai ranar Litinin a babban birnin na jihar watau Fatakwal. Ya bayyan gayyatar da Fubara yawa 'yan majalisar jihar da cewa ta mugunta ce. Okocha yace sun baiwa Gwamna Fubara awanni 48 ya sauka ko a tsigeshi.
Ƴansanda sun kama ƴan bìndìgà su na kokarin sayen ÀĶ-47 a Kano

Ƴansanda sun kama ƴan bìndìgà su na kokarin sayen ÀĶ-47 a Kano

Duk Labarai
Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta kama wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan fashin daji waɗanda ake zargin suna kan hanyarsu ta sayen bindigar AK-47. Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna, ya tabbatar da cafke waɗanda ake zargin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar. A cewarsa, rundunar ta samu gagarumar nasara a kokarinta na dakile yaduwar ‘yan fashin daji da miyagun laifuka a jihar. Ya ce, “A ranar 6 ga Maris, 2025, da misalin karfe 2:00 na rana, wata tawagar jami’an bincike na ‘yansanda ƙarƙashin jagorancin SP Ahmad Abdullahi, jami’in da ke kula da ofishin 'yansanda na Jar Kuka, sun cafke wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan bindiga a gidan man Chula dake Hotoro a Kano. “Waɗanda aka kama sun haɗa da Shukurana Salihu, mai shekara 25; Rabi’u Dahiru, mai s...
Wane Irin Mulki Ake a kasarnan? Kasa da shekaru 2 da kama mulki har an fara yiwa Shugaba Tinubu yakin neman zaben 2027

Wane Irin Mulki Ake a kasarnan? Kasa da shekaru 2 da kama mulki har an fara yiwa Shugaba Tinubu yakin neman zaben 2027

Duk Labarai
Yayin da har yanzu gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata cika shekaru 2 da kafuwa ba, an fara yakin neman zaben 2027 dan ganin ya zarce. Duk da yake shi shugaban kasar ko Jam'iyyar APC a hukumance basu bayyana fara yakin neman zaben ba. Amma wasu jigo a Gwamnatin irin su shugaban Jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Sakataren Gwamnati, George Akume sun bayyana neman Shugaba Tinubu ya zarce. A yayin da yake ganawa da wasu 'yan Jam'iyyar a hedikwatar Jam'iyyar dake Abuja, Ganduje yace 'yan siyasa masu son tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2027 su dakata sai bayan 2031 idan Tinubu ya gama wa'adinsa na shekaru 8 akan mulki. Hakanan shima Akume a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV yace yace Atiku Abubakar ya dakata da neman zama shugab...
Duk da Matatar Dangote, da ta Warri na aiki, yawan tataccen man fetur da ake shigo dashi daga kasar waje ya nunka

Duk da Matatar Dangote, da ta Warri na aiki, yawan tataccen man fetur da ake shigo dashi daga kasar waje ya nunka

Duk Labarai
Rahotanni sun nuna cewa, duk da cewa a yanzu akwai matatun man fetur dake tace mai a gida Najeriya, amma a shekarar 2024, yawan tataccen man fetur din da ake shigo dashi daga kasar waje ya nunka. Rahoton hukumar kididdiga ta kasa, NBS ya bayyana cewa, kudin da ake kashewa dan shigo da man fetur din ya nunka inda yake a kaso 105.3 cikin 100 kamar yanda rahotanni suka nunar. Inda a shekarar 2023 an kashe Naira N7.51tn wajan shigo da man fetur din amma a shekarar 2024 Naira N15.42tn ne aka kashe wajan shigo da tataccen man fetur din daga kasashen ketare. Hakan na zuwane yayin da ake tsammanin cewa za'a samu raguwar dogaro da kasashen waje wajan siyen tataccen man fetur din musamman ma ganin matatar Dangote tana aiki hakanan an tayar da wasu matatun man fetur na Gwamnati.