Wannan wani sanata ne da ya sha da kyar a hannun mutanen mazabarsa a jihar Naija.
Sanatan dan jam'iyyar APC ne, a Bidiyon da ya karade kafafen sada zumunta, An ganshi zagaye da jami'an tsaro.
https://twitter.com/i/status/2045139767776412035
Wannan wani Bidiyo Tauraruwar fina-finan Hausa, Fiddausi Yahya ne dake ta yawo a kafafen sada zumunta.
An ganta a wata kalar shiga i da mutane da yawa ke cewa bata dace ba.
Wasu masoyanta kuma sun rika bayyana cewa, AI ne.
https://www.tiktok.com/@voice_of_k40/video/7629125692801682708?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7629125692801682708&source=h5_m×tamp=1776420710&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=fcc70fdb-731e-4c9b-b7d5-ad5f3ea9960...
Wata daliba ta dauki hankula bayan da aka ga an hanata rubuta jarabawar JAMB saboda ta saka Hijabi.
An ga dalibar a layi, saidai da aka zo kanta, masu binciken sun koreta daga wajan rubuta jarabawar.
Lamarin dai ya dauki hankula inda da yawa suka yi Allah wadai.
https://twitter.com/i/status/2045029498664505433
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Juma'a, 17 ga watan Afrilun shekarar 2026 ya farane a farashin 1340.88.
A yau dai bamu samu farashin kasuwar bayan fage ba.
Wani Bidiyo Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso nata yawo a kafafen sada zumunta inda aka ga yana magana akan cewa yayiwa Peter Obi mataimaki.
Kwankwaso yace yafi Peter Obi komai daga ilimi, Shekaru, da rike mukaman Gwamnati da sauransu.
https://twitter.com/i/status/2044785946210537481
Wani Bidiyo na ta yawo a kafafen sada zumunta inda aka ga wasu awaki na cin fastar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Lamarin ya dauki hankula inda akai ta muhawara akai.
https://twitter.com/i/status/2044804293589643351
Bidiyon ya bayyana kan yanda mutane suka daka wawar fastoci da katakan da aka yi amfani dasu a wajan taron yakin neman zaben shugaba Tinubu a jihar Bayelsa.
Bidiyon da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga mata da maza na wawar fastocin da katakan kowa yana daukar nasa.
Lamarin ya jawo zazzafar muhawara.
https://twitter.com/i/status/2044737240698351839
A zaman kotun dake Abuja da aka yi a yau, Alhamis 16 ga watan Afrilu na ci gaba da shari'ar tsohuwar ministar Jinkai, Sadiya Umat Frouk.
Sadiya da dayan wanda ake zargin me suna Bashir Nura Alkali wanda shine babban sakatare a ma'aikatar basu samu halarta ba.
Na ukunsu, Sani Nafiu Mohammed ne kadai ya samu halartar zaman kotun.
Dan hakane kotun tace a kamosu duk inda suke.
Ana dai zarginsu ne da sama da fadi da wasu rarar kudade na dala Miliyan $1.3 wanda ya kamata a ce an mayar da kudaden asusun gwamnati amma sai suka saka a aljihunsu.
Sannan akwai wasu kudaden suma da suka kai Naira N746,574,303 da ake zarginsu da sacewa.
Jimulla ana musu zarge-zarge guda 21.
Ita dai Sadiya ta bayyana cewa ta je neman lafiya ne kasar Saudiyya shiyasa aka jita shiru.
Rahotanni sun bayyana cewa, Jam'iyyar ADC reshen Wike zasu maka jam'iyyar ADC a kotu.
Shugaban bangaren su Wike, Hon. Abdulrahman Muhammed ne ya bayyana hakan.
Yace yaji ana maganar wai PDP zata hade da jam'iyyar ADC.
Yace wannan ba gaskiya bane kuma suna gargadin ADC ta daina wannan magana idan ba haka ba zasu maka ta a kotu.