Saturday, April 26
Shadow
Tinubu be yi abinda za’a sake zabensa ba, Masu zagina dan na kaiwa Buhari ziyara bakaken Munafukaine>>Atiku Abubakar

Tinubu be yi abinda za’a sake zabensa ba, Masu zagina dan na kaiwa Buhari ziyara bakaken Munafukaine>>Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata cika Alkawuran data daukarwa 'yan Najeriya ba. Yace dan haka bata cancanci a sake zabenta ba. Ya bayyana hakane bayan komawar wasu 'yan PDP jam'iyyar APC inda yace ko a jikinsa. Hakanan Atiku yace masu sukarsa game da ziyara da ya kaiwa tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari munafukaine. Yace Buhari tsohon shugaban kasa ne kuma me ruwa da tsaki a siyasar Najeriya. Yace a lokacin da ya rika kaiwa Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ba'a rika zaginsa ba sai da ya ziyarci Buhari.
An yi zargin cewa, Saida Hamisu Breaker yayi mankas da wìwì kamin yayi wakar Amanata da Hizbah ta Haramta sauraro

An yi zargin cewa, Saida Hamisu Breaker yayi mankas da wìwì kamin yayi wakar Amanata da Hizbah ta Haramta sauraro

Duk Labarai
Wakar Amanata ta Hamisu Breaker na ci gaba da yaduwa sosai duk da haramcin hukumar Hisbah ta Kano. Wani sharhi da masu sauraren wakar ke yi shine, suna zargin cewa Sai da Hamisu Breaker yayi Mankas da Wiwi kamin yayi wakar. Hakan baya rasa nasaba da yanayin wakar, yayi ta a hankali kamar yana jin bacci. https://www.tiktok.com/@zarahsventures/video/7496587920493645111?_t=ZM-8vqkHwpDMG5&_r=1 https://www.tiktok.com/@meenal_shuarah/video/7496971621207608582?_t=ZM-8vqkL9n9mR5&_r=1 https://www.tiktok.com/@autarmommah0/video/7495503950297271558?_t=ZM-8vqkR6r75mv&_r=1 Mata dai na ci gaba da hawa wakar Amanata duk da hanin Hizbah.
Hotuna: Malam Abdullahi Adamu Kahutu Kenan, Babban Yayan Mawaki Rarara A Hanyar Zuwa Aurensa Rarara A Garin Maiduguri A Jiya

Hotuna: Malam Abdullahi Adamu Kahutu Kenan, Babban Yayan Mawaki Rarara A Hanyar Zuwa Aurensa Rarara A Garin Maiduguri A Jiya

Duk Labarai
Malam Abdullahi Adamu Kahutu Kenan, Babban Yayan Mawaki Rarara A Hanyar Zuwa Aurensa Rarara A Garin Maiduguri A Jiya. A jiya Juma'a ne dai aka daura auren Dauda Kahutu Rarara da amaryarsa, Aisha A Birnin Maiduguri na jihar Borno. Rahotanni sun ce Rarara ya biya sadakin Naira 500,000 sannan kuma ya yiwa A'isha Humaira Akwatuna 50.
EFCC ta yi gargadin a yi hattara da fasto bayan da ya nemi a biyashi Naira Miliyan 30 dan ya rikawa koyawa mutane yanda zasu inganta rayuwarsu

EFCC ta yi gargadin a yi hattara da fasto bayan da ya nemi a biyashi Naira Miliyan 30 dan ya rikawa koyawa mutane yanda zasu inganta rayuwarsu

Duk Labarai
Wani fasto me suna Stephen Akintayo ya nemi mutane su biyashi dala 18,000 dan ya koya musu yanda zasu inganta rayuwarsu. Lamarin ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta saboda kudin a Naira sun kai kwatankwacin Naira Miliyan 30. Faston yace da farko mutum zai fara bayar da Naira Miliyan 2.5 kamin daga baya sauran kudin ya rika badasu a hankali har zuwa karshen shekara. Saidai hukumar EFCC ta bakin kakakinta, Dele Oyewale ta gargadi mutane su yi hattara da irin wannan yaudarar. Hakanan shima Mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore ya gargadi mutane da cewa su yi hattara da inda suke saka kudinsu.
DA ƊUMI-ƊUMI: Rahotanni sun ce kimanin akwatin lefe 50 Mawaki Rarara ya yiwa Amaryarsa A’isha Humaira.

DA ƊUMI-ƊUMI: Rahotanni sun ce kimanin akwatin lefe 50 Mawaki Rarara ya yiwa Amaryarsa A’isha Humaira.

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni sun ce kimanin akwatin lefe 50 Mawaki Rarara ya yiwa Amaryarsa A'isha Humaira. https://www.tiktok.com/@arewa_tiktok_com/video/7497204689579117879?_t=ZM-8vqhFiip2s2&_r=1 Mene ne ra'ayoyin ku?
Muma dai Muna goyon bayan a baiwa ‘yan Najeriya damar rike Bìndìgà dan su kare kansu tunda dai jami’an tsaro sun gaza>>Sowore da Solomon Dalung

Muma dai Muna goyon bayan a baiwa ‘yan Najeriya damar rike Bìndìgà dan su kare kansu tunda dai jami’an tsaro sun gaza>>Sowore da Solomon Dalung

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon ministan matasa da wasanni, Solomon Dalung da Dan takarar shugaban kasa kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore sun nemi a baiwa 'yan Najeriya damar rike Bindiga dan su kare kansu. Sunce idan aka yi hakan za'a daina kashe-kashen da ake yi a jihohin Benue da Filato da sauransu. Sun bayyana hakanne a wata ganawa da suka yi da manema labarai a Abuja. Hakan na zuwane watanni 5 bayan da Sanata Ned Nwoko ya kai kudirin neman a baiwa mutane damar rike makamai ...
Kalli yanda aka kama wasu na cinikin sassan jìkìn mutane

Kalli yanda aka kama wasu na cinikin sassan jìkìn mutane

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Ogun a karkashun rundunarsu ta SWAT sun kama wasu mutane da ake zargin suna safarar sassan jikin mutane. Da farko dai an kama Sunday Akintobi dan kimanin shekaru 36 a Itoku ta garin Abeokuta inda daga baya kuma aka kama karin mutane 2 Oladimeji Olaniran dan shekaru 40 da kuma Isaiah Tijani dan shekaru 38. Kakakin 'yansandan jihar, CSP Omolola Odutola, ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an gano wasu abubuwa a gidajen wadannan mutane wanda an yi amannar cewa sassan jikin mutanene. Yace kwamishinan 'yansandan jihar ya bayar da umarnin yi bincike kan lamarin.
Ni zan shiga gaba in jagoranci sojojina mu je mu yi rugu-rugu da Iran idan bata bamu hadin kai wajan tattaunawar hanata mallakar makamin kare dangi ba>>Inji Shugaban Amurka, Donald Trump

Ni zan shiga gaba in jagoranci sojojina mu je mu yi rugu-rugu da Iran idan bata bamu hadin kai wajan tattaunawar hanata mallakar makamin kare dangi ba>>Inji Shugaban Amurka, Donald Trump

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya ce da kansa zai jagoranci yaki da Iran idan tattaunawar da ake yi da kasar bai cimma matsaya ba na kokarin hanata mallakar makamashin kare dangi ba. Yace ba zasu bari Iran ta mallaki makamin ba. Inda ya zargi tsohon shugaban kasar, Joe Biden da barin Iran ta samu tarin arziki. Da aka tambayeshi ko Shugaban kasar Israela, Benjamin Netanyahu zai iya sawa ya shiga yaki da Iran ba tare da ya shirya ba? Trump yace a'a, yace yafi son a samu matsaya maimakon yaki amma idan ba'a cimma matsaya ba zai yi yaki da Iran.
Ji yanda aka kama wasu da suka sàcè yaro me shekaru 6 suka yi gùndùwa-gùndùwa dashi dan yin tsafin samun kudi a jihar Gombe

Ji yanda aka kama wasu da suka sàcè yaro me shekaru 6 suka yi gùndùwa-gùndùwa dashi dan yin tsafin samun kudi a jihar Gombe

Duk Labarai
A jihar gombe, jami'an 'yanssnda sun kama wasu mutane 8 da ake zargi da hannu a cikin yin garkuwa da kashe wani yaro dan shekaru 6. Wadanda ake zargin sun sae yaronne me suna Muhammad Ibrahim Bulama daga gidan kakansa. Sannan suka masa yankan rago suka raba gawarsa gida biyu suka kaiwa wani matsafi da yace zai musu asirin kudi. Wadanda ake zargin sune Magaji Adamu (Wazam), 45, Babayo Musa, 18 years, Jibrin Muhammad (Alias Ya’Haji), 40, Usman Abubakar Khalla, 37, Sadam Umaru, 28, Idris Dayyabu, 45, Abdulrauf Hussaini, 33,Isiyaku Muhammad, 39. Dukansu sun amsa zarge-zargen da ake musu. Kakakim 'yansandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace zasu ci gaba da bincike da tabbatar cewa an yiwa wadannan mutane hukuncin da ya dace dasu.
Kalli Bidiyo: Tauraron fina-finan Hausa, Horo Dan Mama na shan Tofin Allah Tsine saboda cewa Sheikh Bala Lau ya fito da hujja ya kare kansa kan zargin da ake mass

Kalli Bidiyo: Tauraron fina-finan Hausa, Horo Dan Mama na shan Tofin Allah Tsine saboda cewa Sheikh Bala Lau ya fito da hujja ya kare kansa kan zargin da ake mass

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Abdullahi Dan Mama wanda aka fi sani da Horo Dan mama na ci gaba da shan tofin Allah tsine bayan da yayi kira ga shugaban Izala, Sheikh Bala Lau ya fito ya kare kansa kan zargin da ake masa. Horo Dan mama ya wallafa Bidiyon ta sigar barkwanci yana kira ga Sheikh Bala Lau ya fito da takardu a yi bincike kan lamarin zargin da ake masa. https://www.tiktok.com/@horodanmama3/video/7496234447457570103?_t=ZM-8vq7Bfl2rDC&_r=1 Saidai da yawa sun mai Allah wadai da wannan abu da yayi.