Sunday, July 12
Shadow
Kalli Bidiyon: Ko kun saurari sabuwar wakar da Sani Musa Danja yawa yawa DSP Barau data jawo cece-kuce?

Kalli Bidiyon: Ko kun saurari sabuwar wakar da Sani Musa Danja yawa yawa DSP Barau data jawo cece-kuce?

Duk Labarai
Wata sabuwar waka da Sani Musa Danja yawa mataimakin kakakin majalisar Dattijai, Sanata Barau Jibrin ta dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta. Da yawa dai sun bayyana cewa wakar bata da fasali kuma babu basira a yanda aka rera ta. https://www.tiktok.com/@sanidanja/video/7660313778264853780?_r=1&_t=ZS-97wEBm0Pgd3 https://www.tiktok.com/@shariff_auwal844/video/7660946651007405333?_r=1&_t=ZS-97wEzdkCTRt https://www.tiktok.com/@aminujtown/video/7661000468193135890?_r=1&_t=ZS-97wF7zu2OVY https://www.tiktok.com/@dankudakabo/video/7660762538463808789?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7660762538463808789&source=h5_m&timestamp=1783755734&user_id=7483197776647635989&se...
Da Duminsa: A karshe dai Malamin jami’ar nan da ake zargi da neman matar aure ya fito ya fadi nasa bangaren

Da Duminsa: A karshe dai Malamin jami’ar nan da ake zargi da neman matar aure ya fito ya fadi nasa bangaren

Duk Labarai
Malamin Jami'ar da ake zargi ya nemi matar aure a Kano har aka masa na jaki ya fito ya bayyana bangarensa abinda ya faru. Malamin yace wallahi sharri aka masa bai yi lalata da matar ba. Yace asalima itace ta bayyana masa cewa, wai su je su yi soyayyar Ice Cream. Yace har turanci ta masa duk da shi malami ne amma bai taba jin irin wannan Turancin ba. Yace itace ta gaya masa cewa su je wani gidan cin abinci amma yaki yadda yaje. Malamin ya kara da cewa Allah ya taimaka a cikin BUK ne abin ya faru wajene na masu ilimi amma da a wajene Allah kadai yasan me za'a masa. https://twitter.com/i/status/2075706702406529510
Kalli Bidiyon: An sake yiwa wasu mutane 2 Kazafi aka musu irin aika-aikar da akawa Ummulkhairi a wani kauye dake kusa da Maraban Jos, Kaduna

Kalli Bidiyon: An sake yiwa wasu mutane 2 Kazafi aka musu irin aika-aikar da akawa Ummulkhairi a wani kauye dake kusa da Maraban Jos, Kaduna

Duk Labarai
A yayin da ake tsaka da jimamin Abunda Fusatattun matasa sukawa malamar Islamiya Ummulkhairi a Maraban Jos, Jihar Kaduna. An sakewa wasu mutane 2 irin wannan aika-aika a kauyen Unguwan dake kusa da maraban jos Kaduna. Rahoton yace mutanen biyu sun ari sabon mashinne inda suka tafi Zaria akai dan yin wata ziyara, shine suka bi ta kauyen. Mutanen garin na ganin su aka fara musu ihun barayi aka tare aka musu aika-aika aka binne gawarsu, kuma wani abin mamaki shine dattawan garin sun san an aikata hakan amma suka yi shiru. Kakakin 'yansandan jihar Kaduna, DSP Mansur ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun kama mutane 6 da ake zargi a lamarin. https://www.tiktok.com/@agg_multimedia_services/video/7660933734547442952?_r=1&_t=ZS-97vWDrob9YS
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Yanda Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ke taka rawa sosai yana murna bayan da shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa shine zai masa mataimaki a 2027

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Yanda Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ke taka rawa sosai yana murna bayan da shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa shine zai masa mataimaki a 2027

Duk Labarai
A yau ne dai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya tabbatar da cewa, Kashim Shettima ne zai matasa mataimaki a karo na biyu a zaben 2027 A wani Bidiyo daya bayyana a kafafen sadarwa, an ga Mataimakin shugaban kasar nata tika rawa yana murnar wannan lamari. https://twitter.com/i/status/2075658496314310825 Hakanan an ga yanda Kashim Shettima ya je ofis ya gaishe da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kuma yi masa Godiya. https://twitter.com/i/status/2075649231004528940
Da Duminsa: An bayyana randa Gwamnati zata saki Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Da Duminsa: An bayyana randa Gwamnati zata saki Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC ta bayyana sanda Gwamnatin APC zata saki Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Jam'iyyar ta bayyana hakane ta bakin me magana da yawunta, Bolaji Abdullahi a wata hira da yayi da manema labarai Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa, Gwamnatin APC tana sone sai bayan zabe sannan ta saki Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Saboda tasan idan ta sakeshi a yanzu, 'yan Adawa zasu kara karfi.
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya gabatar da  fom dinsa na takara bayan ya cike ga jam’iyyar APC inda kuma ya bayyana Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya gabatar da fom dinsa na takara bayan ya cike ga jam’iyyar APC inda kuma ya bayyana Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mayarwa da jam'iyyar APC fom din takarar shugaban kasa bayan ya kammala cikawa. Sannan ya bayyana Kashim Shettima a matsayin abokin takarar sa na zaben shekarar 2027. Me baiwa shugaban kasar shawara akan harkokin Siyasa, Ibrahim Masari ne ya wakilci shugaban kasar wajan mika wannan fom. https://twitter.com/i/status/2075624224241090932
Da Duminsa: Mansurah Isah tawa Rarara wankin babban Bargo tace ta bar Triple R kuma ya kiyayeta shi da yaransa in ba haka ba idan ta fara tone-tone ba za’a ji dadi ba

Da Duminsa: Mansurah Isah tawa Rarara wankin babban Bargo tace ta bar Triple R kuma ya kiyayeta shi da yaransa in ba haka ba idan ta fara tone-tone ba za’a ji dadi ba

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah Ta bayyana cewa, Ta bar tafiyar Triple R ta Rarara amma ta ji kananan maganganu suna biyowa baya. Ta yi gargadin cewa, idan aka ci gaba zata yi tone-tone. Sannan tace Yanda suka yi da Rarara shine yace mata ta zaba ko shi ko dan shugaban kasa, shine tace ta zabi dan Shugaban kasa. Saidai a kasan shafin Mansurah Isah Matar Rarara tace Mansurah me yasa ta kira sunanta dan ita bata ga abinda ya hadata da ita ba.
Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Mata 4 sun fitar da update din malamin jami’ar da akawa na jaki saboda neman matar aure

Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Mata 4 sun fitar da update din malamin jami’ar da akawa na jaki saboda neman matar aure

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wasu mata 4 sun fito suma sun bayyana cewa malamin jami'ar MAUN dake Kano da aka lakadawa na jaki saboda zargin neman matar aure suna ya nemesu. Matan sun bayyana hakane ga shahararren mawallafin labarai na kafafen sada zumunta, watau, Abis Fulani. Saidai Abis Fulani yace ba zai wallafa zargin da wadannan matan suka kai masa ba inda yace baya son shafinsa ya zama wajan tone-tonen Asirin mutane. Yace matan su kaiwa hukumar makarantarsu korafi. Sannan ya bayyana cewa jami'ar MAUN dake Kano ta fitar da bayanai cewa malamin da aka lakadawa dukan ya daina mata aiki dama aikin wucin gadi ne ya mata. https://www.tiktok.com/@abis_fulani/video/7660643441885416736?_r=1&_t=ZS-97uiA4u0IHl