Saturday, May 17
Shadow

Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’>>Gwanati ta mayarwa Peter Obi Martaninkan cewar da yayi talauci ya karu

‘Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’ — Sanwo-Olu ya kalubalanci Obi kan maganganunsa a jami’a a Amurka.

Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Legas, ya soki Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a 2023, kan maganganun da ya yi game da hauhawar talauci a Najeriya.

A ranar Alhamis da ta gabata, Obi, tsohon gwamnan Anambra, ya yi jawabi a jami’ar Johns Hopkins a Amurka kan taken: ‘Siyasa da Sauyi a Najeriya’.

A cikin jawabin, Obi ya bayyana cewa Najeriya na da mafi yawan talakawa fiye da Indonesia, China da Vietnam. Obi ya wallafa wani ɓangare na jawabin nasa a shafin X.

Sanwo-Olu, a cikin wata sanarwa, ya soki Obi kan “mugun ɗabi’a” da ke “ɓata suna da darajar Najeriya a idon duniya.”

Karanta Wannan  Da Duminsa: A karin Farko Gwamnatin tarayya tace zata tura dan Najeriya na farko zuwa duniyar wata

Gwamnan Legas ya ce la’akari da abin da Obi ya cimma lokacin da yake gwamna, bai cancanci ya soki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *