Wednesday, April 29
Shadow

Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’>>Gwanati ta mayarwa Peter Obi Martaninkan cewar da yayi talauci ya karu

‘Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’ — Sanwo-Olu ya kalubalanci Obi kan maganganunsa a jami’a a Amurka.

Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Legas, ya soki Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a 2023, kan maganganun da ya yi game da hauhawar talauci a Najeriya.

A ranar Alhamis da ta gabata, Obi, tsohon gwamnan Anambra, ya yi jawabi a jami’ar Johns Hopkins a Amurka kan taken: ‘Siyasa da Sauyi a Najeriya’.

A cikin jawabin, Obi ya bayyana cewa Najeriya na da mafi yawan talakawa fiye da Indonesia, China da Vietnam. Obi ya wallafa wani ɓangare na jawabin nasa a shafin X.

Sanwo-Olu, a cikin wata sanarwa, ya soki Obi kan “mugun ɗabi’a” da ke “ɓata suna da darajar Najeriya a idon duniya.”

Karanta Wannan  Najeriya ce ke ƙérą wa Ƙásąŝheɲ Afirka mąkâmäi - inji Matawalle

Gwamnan Legas ya ce la’akari da abin da Obi ya cimma lokacin da yake gwamna, bai cancanci ya soki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *